No menu items!

Sample Page Title

Date:

Amurka ta sake yin gyaran fuska a cikin wani daftarin ƙudiri na Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya don goyan bayan “tsagaita wuta nan da nan na kusan makonni shida a Gaza tare da sakin dukkan waɗanda aka yi garkuwa da su,” a cewar labarin da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani.

Bita ta uku ta rubutun – wacce da farko Amurka ta gabatar makonni biyu da suka gabata – yanzu tana nuna kaifafan maganganun da Mataimakiyar Shugaban Ƙasa Kamala Harris ta yi.

Daftarin farko na Amurka ya nuna goyon baya ga “tsagaita wuta na wucin gadi” a cikin kisan gillar da Isra’ila ta yi a yankin Falasɗinawa da ta yi wa ƙawanya.

KU KUMA KARANTA: Adadin waɗanda suka mutu a Gaza ya haura 30,534 yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare

Amurka na son duk wani goyon bayan kwamitin sulhu na tsagaita wuta ya kasance yana da alaka da sakin mutanen da aka yi garkuwa da su a Gaza.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...