Connect with us

Ƙasashen Waje

Amurka da Birtaniya sun ƙaddamar da hare-hare kan ‘yan tawayen Houthi na Yemen

Published

on

Sojojin Amurka da na Birtaniya sun kai hare-hare a yankunan ‘yan tawayen Houthi na Yemen, inda suka yi amfani da jiragen ruwan yaƙi wurin harba makamai masu linzami samfuran Tomahawk tare da jiragen sama na yaƙi.

Sojojin sun kai hare-hare a wuraren da suka haɗa da ma’ajiyar makamai da na’urorin kare hare-hare ta sama, a cewar jami’an gwamnatin Amurka ranar Juma’a da safe.

Waɗannan hare-hare su ne karon farko da Amurka ta yi martani kan ‘yan tawayen Houthi waɗanda suka daɗe suna yin amfani da jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami wajen kai hari kan jiragen ruwa na ɗaukar kaya da ke zuwa Isra’ila tun lokacin da aka ƙaddamar da hare-hare a Gaza.

Shugaban Amurka Joe Biden ya ce hare-haren da suka kai Yemen sun nuna cewa ƙasarsa da ƙawayenta ba za su “lamunci” hare-haren da ‘yan tawayen Houthi suke kai wa jiragen ruwansu ba.

KU KUMA KARANTA: Biden ya ce Amurka ba za ta bari a tursasa wa Falasɗinawa fita daga Gaza ba

A wata sanarwa da ya fitar, Biden ya ce a karon farko sun yi amfani da makamai masu linzami na ruwa wajen kai hare-hare kan ‘yan tawayen Houthi domin yin raddi game da jerin hare-haren da suke kai wa jiragen ruwa da ke wucewa ta Bahar Maliya.

A gefe guda, shugaban Houthi Ali al-Qahoum ya ce sun ƙaddamar da hare-hare kan jiragen yaƙin Amurka da Birtaniya da ke Bahar Maliya domin yin martani kan hare-haren da aka kai musu.

“Amurkawa da Masu kishin Yahudawa da Birtaniya da ke yaƙi da Yemen sun ƙaddamar da jerin hare-hare a babban birnin, Sanaa, da yankin Hudaida da Saada, da kuma Dhamar,” a cewar wani jami’in Houthi Abdul Qader al Mortada a sakon da ya wallafa a shafin X.

Wakilan kamfanin dillancin labarai na Associated Press journalists a Sanaa sun ce sun ji ƙara huɗu ta fashewar wasu abbuwa amma ba su ga alamar jiragen yaƙi ba.

Mutum biyu mazauna Hudaida, Amin Ali Saleh da Hani Ahmed, sun ce sun ji ƙara guda biyar ta fashewar bama-bamai. Hudaida yanki ne da ke tsakanin Bahar Maliya kuma shi ne birni mafi girma mai tashar jiragen ruwa da ke ƙarƙashin Houthi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Published

on

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Daga Ibraheem El-Tafseer

Me magana da yawun Shelkwatar zaɓe ta Iran Dakta Muhsin Elsami, ya sanar da cewa, an kammala lissafi ƙuri’a Miliyan 25 na zaɓen shugaban ƙasar Iran wanda aka fara ranar juma’a.

‘Yan takara 6 ne suka tsallake matakin ƙarshe yayin da 2 suka fice saboda ra’ayin kai, ana zaɓe saura kwana 2.

Dakta Mas’ud Pezeshkian shi ne kan gaba da ƙuri’a Miliyan 10.415.991

Dakta Sa’ed Jalili ya samu ƙuri’u Miliyan 9.473298

Se kuma Dakta Qalibaf ya samu ƙuri’a Miliyan 3.383.340

Sai Ayatullah Musfata ya samu ƙuri’a 206.397.

Yanzu haka an fitar da Dakta Baqir Qalibaf da Ayatullah Musfata da suke da ƙarancin ƙuri’a, ya rage saura Dakta Jalili da Dakta Mas’ud Pezeshkian da ken gaba.

KU KUMA KARANTA: Iran ta tabbatar da mutuwar shugaban ƙasar, Ebrahim Ra’isi, a hatsarin jirgin sama

Jami’i Muhsin Elsami ya sanar da cewa za’a shiga matakin zaɓe na 2 ranar Juma’a mai zuwa inda za a kara tsakanin Dakta Jalili da Dakta Mas’ud.

Cikin su duk wanda ya samu kaso 50 ya zama shugaban ƙasar Iran, wanda zai maye gurbin Shahid Ebrahim Ra’isi wanda ya rasu sanadiyyar hatsarin jirgin Helikofta, a watan da ya gabata.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra’ila kan Shugaba Erdogan

Published

on

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra'ila kan Shugaba Erdogan

Turkiyya ta yi tur da kalaman ministan Isra’ila kan Shugaba Erdogan

Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta yi Allah wadai da wani saƙo da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila, Israel Katz ya wallafa a shafukan sada zumunta a baya-bayan nan kan shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, inda ta bayyana hakan a matsayin wani yunƙuri na Isra’ila na ɓoye laifukanta.

Sanarwar da Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta fitar a ranar Talata ta ce “Muna daukar wannan matsayi na rashin mutuntawa da Ministan Harkokin Wajen Isra’ila ke yi wa mai girma shugaban kasarmu a matsayin wani lamari da za a ji shi ne kawai daga bakin ƙasar da ake zarginta da kisan kiyashi.”

Yayin da take suka da kakkausar murya a shafukan sada zumunta, ma’aikatar ta ce: “Irin wannan ƙazafi da ƙarya wani ɓangare ne na ƙoƙarin Isra’ila na ɓoye laifukan da ta aikata.”

Turkiyya ta ƙara da cewa, za ta ci gaba da fafutukar tabbatar da zaman lafiya da adalci.

KU KUMA KARANTA: Ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza – Ministan Turkiyya

Isra’ila, wadda ta yi fatali da ƙudurin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ke neman tsagaita wuta cikin gaggawa, ta fuskanci tofin Allah-tsine a tsakanin kasashen duniya a ci gaba da kai munanan hare-hare kan Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Fiye da Falasɗinawa 37,700 aka kashe tun daga lokacin a Gaza, yawancinsu mata da yara, kuma kusan wasu 86,400 sun jikkata, a cewar hukumomin lafiya na yankin.

Sama da watanni takwas da yakin Isra’ila a Gaza, inda yankuna da dama suka zama kufai a cikin yankin da aka yi wa ƙawanya da hana shigar da abinci da ruwan sha da magunguna.

Ana tuhumar Isra’ila da aikata kisan kiyashi a Kotun Duniya, wanda hukuncin na baya-bayan nan ya umarci Tel Aviv da ta dakatar da kai hare-hare a kudancin birnin Rafah, inda Falasɗinawa sama da miliyan guda suka nemi mafaka daga yakin kafin a mamaye shi a ranar 6 ga watan Mayu.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like