Labarai
Amarya da mai juna biyu sun mutu a gobarar matatar mai a Ribas
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/10/vandalised-pipeline.jpg)
Mutane 18 sun mutu, cikinsu har da wata mai juna biyu da wata amarya, sun mutu sakamakon fashewar wata matatar man fetur ba bisa ƙa’ida ba a Jihar Ribas.
Wani jami’in tsaro a yankin ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa mutane da dama sun ƙoƙƙone baya ga mutum 18 da suka mutu a sakamakon bindigar da matarar man ta yi.
Mai magana da yawun hukumar tsaro ta sibil difens (NSCDC) a jihar, Olufemi Ayodele, ya ce, “Da tsakar dare wutar ta fara ci, inda mutane 18 suka mutu, sakamakon sun ƙone ƙurmus, wasu 25 da suka samu raunukan ƙuna kuma an cece su.Ya ce, “Yawancinsu matasa ne, sai wata mai juna biyu da wata mata da ake shirin bikin ɗaurin aurenta a cikin waɗanda a bin ya ritsa da su.”
KU KUMA KARANTA: Fashewar bututun ɗanyen mai yayi sanadiyar mutuwar mutane 12
Mazauna yakin Emohua sun ce adadin waɗanda suka mutun zai iya ƙaruwa saboda akwai waɗanda ke kwasar man da ke tafiya a ƙasa lokacin da gobarar ta tashi.
Wutar ta tashi ne bayan wuta ta kama a rumbun ajiyar mai na matatar, inda ta ƙoƙƙona mutane, ta kashe wasu.
Mazauna yakin Emohua sun ce adadin waɗanda suka mutun zai iya ƙaruwa saboda akwai waɗanda ke kwasar man da ke tafiya a ƙasa lokacin da gobarar ta tashi.
Matsalar fasa bututun mai da tacewa ba bisa ƙa’ida ba ta yi ƙamari a yankin Kudancin Najeriya, inda man da ke gangarawa ta bututun da masu satar man suke amfani da su kan yi bindiga su hallaka mutane.
Al'ajabi
Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas
![Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/building.jpg)
Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas
Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.
Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.
An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.
KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja
Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.
Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.
Labarai
Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja
![Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/EFCC456.jpg)
Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja
Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.
An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.
Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.
An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.
Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.
Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.
Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.
KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja
Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.
Labarai
NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu
![NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240701-WA0014-1-768x576-1.jpeg)
NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu
Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.
Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.
A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.
Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .
Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.
KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J
Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.
Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.
A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano