Connect with us

Labarai

Al’ummar Nguru a jihar Yobe, sun katange unguwannin da ke fuskantar ambaliyar ruwa

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Kamar yadda hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet) ta bayyana cewa, jihar Yobe tana ɗaya daga cikin jihohin da ke fuskantar ambaliyar ruwa a daminar bana. Wannan ne ya sa al’ummar garin Nguru da ke jihar Yobe, musamman unguwannin da suke fuskantar ambaliyar ruwa duk shekara, suka katange unguwannin nasu daga fuskantar ambaliyar ruwa. Wato suka tona ƙaton rami mai zurfi, kamar kwalbati, yadda ko da ruwan ya zo ba zai iya haura wa ba, sai dai ya bi ta wannan ramin ya tafi.

Idan ba a manta ba, a shekarar da ta gabata, unguwar Barma da ke cikin garin na Nguru, inda ambaliyar ruwa ya rushe kusan dukkan gidajen da ke unguwar da gonakinsu da kuma wuraren sana’o’insu. Wanda hakan ya haifar da da yawa suka rasa muhallansu, dole sai da wasu suka yi ƙaura suka bar unguwar.

KU KUMA KARANTA: Ambaliyar ruwa: Gwamnatin Bauchi ta gina sansanonin ‘yan gudun hijira

Wani mazaunin unguwar mai suna Hamza Sulaiman, ya shaida wa manema labarai cewa, “a shekarar da ta gabata mun fuskanci ambaliyar ruwa a wannan unguwa, gidaje da yawa sun rushe gaba ɗaya, ko ɗaki ɗaya bai saura ba. Akwai gidajen da masu gidajen sun gagara tayar da ko ɗaki ɗaya, saboda yanayin halin rayuwa da ake fama da shi” inji shi.

Wasu zaratan matasa ne tare da taimkon ƙaramar hukumar Nguru, suka duƙufa wurin katange unguwannin da ambaliyar ruwan ke yiwa barazana. Ɗaya daga cikin matasan mai suna Mohammed Abubakar ya shaida wa Wakilinmu cewa “ambaliyar ruwan tana damun mu duk shekara a wannan unguwa, wasu ba sa iya kwana a gidajensu, dole sai sun fita sun bar gidajen nasu, saboda ruwan ya cinye gidajen. Shi ya sa muke wannan aiki don kare kanmu daga barazanar ambaliyar ruwa da muke fuskanta”. inji shi

Shugaban ƙaramar hukumar Nguru, Alhaji Madu Kachalla ya bayyana cewa gwamnatin jiha ta gyara magudanan ruwa, sannan an kwashe dattin da ke ciki domin gudun aukuwar ambaliyar ruwan. Sannan ana ci gaba da katange unguwannin da ambaliyar ruwa ke yiwa barazana. Sannan akwai wuraren da ruwa ke taru wa (Kogi), za mu sa a yashe ruwan gaba ɗaya. Idan ba a yashe ruwan ba, idan ruwan saman ya zo, shi ne yake haifar da ambaliyar”. inji Madu Kachalla.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like