Allah Ya yi wa Bintu Daɗin Kowa rasuwa

Allah Ya yi wa jarumar Kannywood, Fatima Sa’ida wadda aka fi sani da Bintu ta shirin Daɗin Kowa rasuwa.

Jarumar ta rasu ne bayan ta sha fama da rashin lafiya.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin jihar Yobe ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu, saboda rasuwar Bukar Abba

Wannan na cikin wani saƙo da Shugaban Hukumar Fina-Finai da Ɗab’i na Jihar Kano, Abba El-Mustapha ya wallafa a shafinsa na Instagram.

Tuni aka yi jana’izarta kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar, a unguwar Gunduwawa da ke Kano.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *