Connect with us

Ƙasashen Waje

Al-Burhan ya ce ba zai sasanta da rundunar RSF ta Sudan ba

Published

on

Shugaban Sojin Sudan Abdel Fattah al-Burhan ya sha alwashin ci gaba da yaƙin da suke yi da rundunar RSF a ƙasar, inda ya yi watsi da buƙatar tsagaita wuta ta baya-bayan nan.

A farkon makon nan ne Shugaban RSF Hamdan Dagalo ya amince da buƙatar tsagaita wuta wadda ƙungiyoyin farar hula suka gabatar, wanda hakan ya ƙunshi idan sojoji sun amince.

Sai dai masu lura da al’amura sun mayar da martani cikin kakkausar murya bisa la’akari da alƙawurran da rundunar ta yi a baya da ba ta cika ba.

Ɓangarorin biyu sun cimma yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta da dama a farkon watannin yaƙin. Sai dai masu ido sun mayar da martani cikin kakkausar murya bisa la’akari da alƙawurran da rundunar ta yi a baya waɗanda ba ta cika ba.

Ɓangarorin biyu sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da dama waɗanda ba su ɗore ba a farkon watannin yaƙin.

KU KUMA KARANTA: Sudan ta kori ma’aikatan jakadancin Chadi daga Khartoum

“Duka duniya ta shaida yadda dakarun ‘yan tawayen nan suka rinka aikata laifukan yaƙi da kuma laifin take hakkin bil adama a Yammacin Darfur da sauran yankunan Sudan.

Sakamakon haka, ba za mu sasanta da su ba, ba mu da wata yarjejeniya da su,” kamar yadda Burhan ya bayyana, wanda shi ne shugaban na Sudan a lokacin da dakarunsa suka taru a birnin Port Sudan.

An soma wannan yakin a ranar 15 ga watan Afrilu inda ya lalata wurare masu yawa a Sudan da kuma raba da sama da mutum miliyan 7.5 da muhallansu.

Ganin cewa RSF ta samu dama a wannan yaƙin, Ƙungiyar Intergovernmental Authority on Development, ta samu Burhan da Dagalo, wanda aka fi sani da Hemedti, a watan da ya gabata, don amincewa da wani taron kai tsaye.

Sai dai Burhan a ranar Juma’a ya yi watsi da hakan inda ya ƙira abokin adawar tasa a matsayin “sakarai”, kuma “matsoraci”.

Ya yi watsi da buƙatar tsagaita wuta da Dagalo ya saka wa hannu a Addis Ababa babban birnin Habasha a wannan makon.

Haka kuma Burhan ya caccaki shugabannin Afirka waɗanda suka haɗa da Habasha da Kenya waɗanda suka karɓi Dagalo a wata ziyara da ya kai a makon nan da kuma wasu ‘yan siyasar Sudan waɗanda suka haɗu da shi a Habasha.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like