Connect with us

DSS

Akwai masu shirin tayar da tarzoma a lokacin rantsar da sabbin gwamnatoci a Najeria – Jami’an DSS

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Hukumar tsaron farin kaya ta ‘yan sandan ciki ta Najeria, (DSS) ta bayyana cewa akwai wasu da suke shirin tayar da zaune tsaye a lokacin bukukuwan miƙa mulki da za a yi a wasu jihohin ƙasar.

A wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis, hukumar ta ce mutanen suna son yi wa aikin jami’an tsaro naƙasu ne tare kuma da tayar da hankalin jama’a su jefa tsoro ga ‘yan ƙasar a lokacin.

A sanarwar wadda kakakinta, Peter Afunanya ya fitar, hukumar ta buƙaci jama’a da ‘yan jarida da ‘yan ƙungiyoyin farar hula da duk wasu masu ruwa da tsaki a harkar da su bi ƙa’idojin da aka tsara a lokacin bikin a ko’ina a faɗin ƙasar.

Haka kuma sanarwar ta shawarci jama’a da su yi watsi da labaran ƙarya ko na ƙanzon-kurege da na zuzuta al’amura da kuma duk wani abu na neman razanarwa.

KU KUMA KARANTA: DSS tayi gargaɗi ga ‘yan siyasar da ke shirin yin zanga zanga a ofishinta

Hukumar ta kuma shawarci duk wani mutum da ba shi da takardar izini ko ta tantancewa da ya kauce wa shiga wasu wuraren a lokacin da ake bikin.

DSS ta bai wa jama’a tabbacin ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin ganin bukukuwan sun wakana lami lafiya cikin nasara a ko’ina a faɗin ƙasar.

A ranar Litinin 29 ga watan nan na Mayu 2023 ne za a yi bikin miƙa mulki da rantsar da sabon shugaban ƙasa a Abuja da kuma gwamnoni a wasu jihohin Najeriyar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

DSS

DSS ta sako wacce ta soki gwamnatin Kaduna a Facebook

Published

on

An sako Aisha Galadima, wacce take kare tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da jami’an tsaron farin kaya (DSS) suka kama don yin bincike.

Aminiya ta ruwaito yadda aka damƙe ’yar Jam’iyyar APC  a Kaduna bisa wani rubutu da ta yi a Facebook kan Gwamna Uba Sani.

A cewar majiyoyi, Aisha Galadima ta soki kalaman Gwamna Uba Sani na ƙarshe a kan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai.

Wata ƙwabciyarta ta ce, an kama ta ne a unguwar Tudun Wada a Kaduna a ranar Lahadi da yamma, kuma wata abokiyarta ta bayyana cewa wayar Aisha a kashe take bayan tsare ta da aka yi.

Sai dai babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan, Muhammad Lawal Shehu, ya ce ba shi da masaniyar kama ta.

“Ban san an kama wata mata da ta rubuta munanan kalamai a kan Gwamna ba. Amma kuna iya mika tambayoyinku ga hukumar DSS ba gwamnatin jihar Kaduna ba,” in ji shi.

KU KUMA KARANTA: El-Rufai ya bar wa jihar Kaduna ɗimbim bashi – Gwamnan Uba Sani

An sake ta ne bayan da ta kai kusan awa 24 a hannun hukuma.

Da aka tuntuɓi Aisha, ta tabbatar da sakin nata, inda ta ce jami’an hukumar sun tursasa tare da dukan ta.

“Ina cikin ɗakina zan yi wanka sai suka shigo suka ja ni. Na ga motar su ƙirar Hilux hudu a wajen gidan. Suka tura ni ciki suka wuce,” in ji ta.

A cewarta, (DSS) sun zarge ta da yin wani rubutu a kan gwamnan a watan Fabrairu.

Continue Reading

DSS

DSS sun cafke shugaban ƙungiyar Miyatti Allah

Published

on

Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta kama shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Bodejo, kan kafa rundunar sa-kai ta Fulani a jihar Nasarawa.

Wasu shugabannin ƙungiyarsa ta Kautal Hore kuma makusanta sun tabbatar da batun kama Bodejo a jiya Talata.

Sun ce jami’an DSS tare da wasu sojojin Najeriya suka kama shi a garin Lafiya babban birnin jihar Nasarawa.

Sai dai sun ce suna bin bahasi domin ba su san inda aka tafi da shi ba.

A ranar Laraba 17 ga watan Janairu Bello Badejo ya ƙaddamar da rundunar a garin Lafiya inda ya ce za ta taimaka wajen yaƙar ɓarayi da ɓata-gari daga cikin Fulani.

KU KUMA KARANTA: An ɗaure Sarkin Fulani da ‘yan uwansa 2 kan garkuwa da mutane

Bayanai na cewa jami’an tsaron Najeriya sun kama Bodejo ne kan fargabar cewa ƙirƙiro da ƙungiyar sa-kai zai iya janyo tashin hankali a faɗin ƙasar, kuma kasancewar ba ta da rijista da hukumar farin kaya ta DSS.

Continue Reading

DSS

DSS ta ce shugabanta bai sace kuɗin tallafi na ma’aikatan hukumar ba

Published

on

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya a Najeriya DSS ta musanta zarge-zargen da ake yi kan cewa babban daraktan hukumar Magaji Yusuf Bichi ya yi sama da faɗi da kuɗin tallafi na ma’aikatan hukumar.

Mai magana da yawun hukumar Peter Afunanya ne ya fitar da sanarwar inda ya musanta zargin da wani Jackson Ude ya yi a shafin X wanda ya yi zargin shugaban DSS din da kwashe kuɗin.

Afunanya ya tabbatar da cewa babu wasu kuɗi da aka bai wa hukumar a halin yanzu domin ma’aikata kuma da zarar an fitar da waɗannan kuɗaɗe za a bai wa ma’aikatan hakkinsu.

“Hukumar tana son sanar da cewa zarge-zargen da ake yi ba gaskiya bane. Hukumar na son tabbatar da cewa daraktan hukumar ko wani mai aiki da umarnin shi, babu a cikinsu wanda ya sace kuɗin tallafin da aka bai wa ma’aikata.

KU KUMA KARANTA: Sojoji da DSS sun daƙile yunkurin Boko Haram na kai hari a Kano

“Babu wani tallafi da aka bai wa hukumar kuma da zarar an bayar da shi, za a bai wa ma’aikatan hakkinsu,” in ji sanarwar.

Hukumar ta DSS ta buƙaci jama’a su yi watsi da ƙarerayin da ake yaɗawa waɗanda ke kawo rabuwar kai da kuma rikici.

Haka kuma hukumar ta tabbatar da cewa daraktan na DSS zai ɗauki matakai na shari’a dangane da lamarin.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like