No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Hukumar tsaron farin kaya ta ‘yan sandan ciki ta Najeria, (DSS) ta bayyana cewa akwai wasu da suke shirin tayar da zaune tsaye a lokacin bukukuwan miƙa mulki da za a yi a wasu jihohin ƙasar.

A wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis, hukumar ta ce mutanen suna son yi wa aikin jami’an tsaro naƙasu ne tare kuma da tayar da hankalin jama’a su jefa tsoro ga ‘yan ƙasar a lokacin.

A sanarwar wadda kakakinta, Peter Afunanya ya fitar, hukumar ta buƙaci jama’a da ‘yan jarida da ‘yan ƙungiyoyin farar hula da duk wasu masu ruwa da tsaki a harkar da su bi ƙa’idojin da aka tsara a lokacin bikin a ko’ina a faɗin ƙasar.

Haka kuma sanarwar ta shawarci jama’a da su yi watsi da labaran ƙarya ko na ƙanzon-kurege da na zuzuta al’amura da kuma duk wani abu na neman razanarwa.

KU KUMA KARANTA: DSS tayi gargaɗi ga ‘yan siyasar da ke shirin yin zanga zanga a ofishinta

Hukumar ta kuma shawarci duk wani mutum da ba shi da takardar izini ko ta tantancewa da ya kauce wa shiga wasu wuraren a lokacin da ake bikin.

DSS ta bai wa jama’a tabbacin ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin ganin bukukuwan sun wakana lami lafiya cikin nasara a ko’ina a faɗin ƙasar.

A ranar Litinin 29 ga watan nan na Mayu 2023 ne za a yi bikin miƙa mulki da rantsar da sabon shugaban ƙasa a Abuja da kuma gwamnoni a wasu jihohin Najeriyar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...