No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Majalisar dattawan Najeriya, Godswill Akpabio ya buƙaci shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya sanyawa ministocinsa takunkumin tafiye-tafiye zuwa ƙasashen ƙetare lokacin da ake kare kasafin kuɗin ma’aikatu.

Akpabio yace irin waɗannan tafiye-tafiye na hana ministocin da shugabannin hukumomin gwamnati bayyana a gaban ‘yan majalisu domin ƙare kasafin kuɗin da suka gabatar da kuma tuhumar da majalisa ke yi a kan wasu ayyukan da ake sakawa.

Shugaban majalisar ya yi alƙawarin cewar zasu bincike kasafin da shugaban ƙasar ya gabatar sosai, kamar yadda kundin tsarin mulki ya basu dama, kafin amincewa da shi.

Akpabio ya kuma buƙaci ɓangaren zartarwar da ya nemo hanyar rage basussukan da ake bin Najeriya, duk da yake sun san cewar wannan gwamnati ta gaji wasu basussukan daga gwamnatin da ta gabace ta.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya gabatar da kasafin kuɗin 2024

Shugaban majalisar ya yi kuma alƙawarin haɗa kai da hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa domin daƙile hanyoyin da jami’an gwamnati ke amfani da su suna karkata dukiyar jama’a.

Wannan shine kasafin kuɗi na farko da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar tun bayan hawansa karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...