Connect with us

Ƙasashen Waje

Afirka ta Kudu ta shigar da ƙara don a ɗauki sabbin matakai a kan Isra’ila

Published

on

Afirka ta Kudu ta shigar da wata buƙatar gaggawa ta neman a ɗauki ƙarin matakai da kuma yin kwaskwarima kan hukuncin da Kotun Duniya ta yanke a kan batun kisan ƙare-dangin da ake tuhumar Isra’ila da shi, kamar yadda Babbar Kotun Majalisar Ɗinkin Duniyar ta faɗa.

A cikin sabuwar buƙatar tata ta gaggawa, Afirka ta Kudu ta ce ta gabatar da ita ne saboda “sababbin bayanan gaskiya da suka ɓullo, da kuma sauye-sauyen da aka samu a halin da ake ciki a Gaza, musamman halin yunwa da ake fama da ita,” in ji wata sanarwa da Kotun Duniyar ICJ ta fitar.

A cewar buƙatar, waɗannan kashe-kashe da Isra’ila ke ci gaba da yi, sun saɓa wa yarjejeniyar kariya da hukunta laifukan kisan ƙare-dangi da kuma keta matakan wucin-gadi da wannan kotun ta bayar a watan Janairu.

Ana tuhumar Isra’ila da laifin kisan kiyashi a Kotun Duniya. Hukuncin wucin-gadi da aka yanke a watan Janairu ya umarci Tel Aviv ta dakatar da kisan ƙare-dangi tare da ɗaukar matakan tabbatar da cewa an ba da taimakon jinƙai ga fararen-hula a Gaza.

KU KUMA KARANTA: Adadin waɗanda suka mutu a Gaza ya haura 30,534 yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare

Munanan hare-hare Isra’ila ta ƙaddamar da wani ƙazamin farmakin soji, wanda yanzu haka aka shiga kwana na 152 tana kai hare-hare a Zirin Gaza, tun bayan harin ba-zata da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba, wanda Tel Aviv ta ce ya kashe kusan mutum 1,200.

Fiye da Falasɗinawa 30,700 aka kashe tun daga lokacin, sannan sama da 72,000 suka jikkata, yayin da ake ta lalata ababen more rayuwa da kuma sanya al’ummar yankin Gaza a cikin halin yunwa.

Har ila yau Isra’ila ta ƙaƙaba wa Zirin Gaza wani shinge da takunkumai, waɗanda suka bar al’ummarta, musamman mazauna arewacin Gaza, cikin halin ha’ula’i.

Yakin Isra’ila ya sa kashi 85 cikin 100 na al’ummar Gaza sun yi gudun hijira a cikin mawuyacin hali sakamakon ƙarancin abinci da ruwa mai tsafta da magunguna, yayin da aka lalata kashi 60 na ababen more rayuwa na yankin, a cewar MƊD.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like