No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani kwamiti na ma’aikatar ilimi mai zurfi ta Afganistan ta ce yana kan shirin sake buɗe jami’o’i ga ɗalibai mata, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na ƙasar suka ruwaito a ranar Litinin.

Kwamitin ya bayyana hakan ne a lokacin wani rahoto na shekara-shekara na ma’aikatar.

“Za mu raba shi da jama’a idan an kammala shirin,” in ji rahoton.

KU KUMA KARANTA: Taliban ta haramta wa matan Afganistan yin kayan kwalliya, da rufe waɗanda ake da su

Muƙaddashin ministan ilimi mai zurfi Lutfullah Khairkhwa ya ce har yanzu ba a bayyana lokacin kammala shirin ba.

Ya zuwa yanzu dai an hana mata shiga jami’o’i a ƙasar Afganistan.

Ma’aikatar Ilimi mai zurfi ta sanar da hana ilimin mata a watan Disamba 2022.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...