Connect with us

Ƙasashen Waje

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Published

on

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Adadin waɗanda suka mutu a tarzomar Kenya ya ƙaru

Ƙungiyar likitoci ta Kenya ta ce adadin waɗanda suka mutu, sanadiyar zanga-zangar ƙarin kuɗin haraji da gwamnatin ƙasar ta sanar, ya ƙaru zuwa 13.

Shugaban Ƙungiyar Simon Kigondu ne ya tabbatarwa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP adadin, a wata zantawa da suka yi da shi a yau Laraba.

Masu zanga-zangar waɗanda yawancinsu matasa ne, sun mamaye zauren majalisar dokokin kasar a jiya Talata, inda suka rinka jifar ‘yan sanda da duwatsu da kuma rushe shingen jami’an tsaro don kutsa kai cikin harabar majalisar.

Bayan faruwar lamarin, shugaban ƙasar William Ruto ya tura da jami’an soji don tarwatsa masu zanga-zangar.

KU KUMA KARANTA: Mutum 12 sun mutu a rikicin da ya biyo bayan zaɓen shugaban ƙasa a Chadi

Shugaba Ruto ya lashi takobin ɗaukar tsauraran matakai don tabbatar da zaman lafiya a ƙasar, inda ya sha alwashin hukunta wadanda ke da hannu a lamarin.

Sai dai duk da ɗaukar wancan mataki, masu zanga-zangar sun ce babu gudu babu ja da baya game da ƙudirinsu na ci gaba da zanga-zangar, har sai haƙarsu ta cimma ruwa.

Wani jami’i a asibitin Kenyatta da ke birnin Nairobi, ya ce a asibitin kadai, jami’insu sun duba mutane 160 da suka samu raunukan harhasai wasu kuma kananan raunuka.

Ɗaya daga cikin abubuwan da masu zanga-zangar ke buƙata shi ne shugaban ƙasar William Ruto ya sauka daga muƙaminsa.

Matasan sun bayyana matakin gwamnatin Ruto na lafta wa jama’a haraji a matsayin wani sabon yunƙuri na jefa al’umma cikin ƙarin musiba, ganin yadda tuni matsalar tsadar rayuwa ta yi musu dabaibayi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Published

on

Isra'ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza

Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar

Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Published

on

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana - COPEC

Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.

Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.

COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.

COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.

Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya

Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.

Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Published

on

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

An kammala zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Iran

Daga Ibraheem El-Tafseer

Me magana da yawun Shelkwatar zaɓe ta Iran Dakta Muhsin Elsami, ya sanar da cewa, an kammala lissafi ƙuri’a Miliyan 25 na zaɓen shugaban ƙasar Iran wanda aka fara ranar juma’a.

‘Yan takara 6 ne suka tsallake matakin ƙarshe yayin da 2 suka fice saboda ra’ayin kai, ana zaɓe saura kwana 2.

Dakta Mas’ud Pezeshkian shi ne kan gaba da ƙuri’a Miliyan 10.415.991

Dakta Sa’ed Jalili ya samu ƙuri’u Miliyan 9.473298

Se kuma Dakta Qalibaf ya samu ƙuri’a Miliyan 3.383.340

Sai Ayatullah Musfata ya samu ƙuri’a 206.397.

Yanzu haka an fitar da Dakta Baqir Qalibaf da Ayatullah Musfata da suke da ƙarancin ƙuri’a, ya rage saura Dakta Jalili da Dakta Mas’ud Pezeshkian da ken gaba.

KU KUMA KARANTA: Iran ta tabbatar da mutuwar shugaban ƙasar, Ebrahim Ra’isi, a hatsarin jirgin sama

Jami’i Muhsin Elsami ya sanar da cewa za’a shiga matakin zaɓe na 2 ranar Juma’a mai zuwa inda za a kara tsakanin Dakta Jalili da Dakta Mas’ud.

Cikin su duk wanda ya samu kaso 50 ya zama shugaban ƙasar Iran, wanda zai maye gurbin Shahid Ebrahim Ra’isi wanda ya rasu sanadiyyar hatsarin jirgin Helikofta, a watan da ya gabata.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like