Connect with us

Labarai

Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Published

on

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa, adadin mutanen da suka rasa muhallansu a sassan duniya ya zarta miliyan 114, adadi mafi girma da majalisar ta tattara a tarihi.

Babbar matsalar da ta raba mutanen da gidajensu a watanni shida na farkon wannan shekara ta 2023, ita ce tashe-tashen hankulan da ake fama da su a Ukraine da Sudan da Somalia da Myanmar da Jamhuriyar Dimokuraɗiyar Congo har ma da rikici a Afghanistan.

Kazalika ibtila’o’in da aka samu na fari da ambaliyar ruwa da rashin tsaro sun taimaka wajen raba mutanen da gidajensu kamar yadda Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijra ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) ta bayyana.

Sanarwar UNHCR ta ce, yanzu haka hankalin duniya ya karkata ne kan yaƙin da ake fama da shi a Zirin Gaza wanda ya cika da ɗimbim fararen hula, amma fa akwai rikice-rikice da dama da ke ci gaba da ta’azzara tare da raba mutane da muhallansu a sassan duniya.

KU KUMA KARANTA: Ta nemi Majalisar Ɗinkin Duniya ta ƙaddamar da yaƙi kan yin hijira ba bisa ƙa’ida ba

Shugaban hukumar, Filippo Grandi ya zargi ƙasashen duniya da gazawa wajen magance tashe-tashen hankula da dama, yana mai buƙatar samar da haɗin kai don kawo ƙarshen matsalar ta raba mutane da muhallansu tare da komar da su gida.

Grandi ya kuma ce, wani kaso na adadin mutane da suka rasa muhalli sun tsere daga gidajensu ne sakamakon matsalar take haƙƙin ɗan Adam da ake fama da ita a wasu sassan.

“Gazawar al’ummomin duniya wajen magance rikice-rikice ko hana aukuwar sabbi shi ne musabbabin rasa muhalli da kuma ƙara jefa waɗanda lamarin ya shafe cikin zullumi.

“Dole ne mu yi wa kanmu karatun ta nutsu, mu yi aiki tare don kawo ƙarshen rikice-rikice, wanda hakan zai bai ’yan gudun hijira da sauran mutanen da suka rasa matsugunansu su koma gida ko kuma su sake gina matsugunansu,” in ji Grandi.

Ya zuwa watan Yuni, adadin mutanen da aka tilastawa gudun hijira a duniya ya kai miliyan 110, wanda wannan wani ƙari ne kan mutum miliyan 1.6 da suka tsere daga muhallinsu a rahoton da aka fitar a ƙarshen shekarar 2022.

Haka kuma, a tsakanin watan Yuni zuwa ƙarshen watan Satumba, an ƙiyasta ƙarin wasu miliyan huɗu da aka tilastawa gudun hijira, wanda ya kawo adadin zuwa miliyan 114.

Rahoton na UNHCR bai ƙunshi alƙaluman rikicin Isra’ila da Falasɗinu ba wanda ya ɓarke a ranar 7 ga Oktoba ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like