Connect with us

Ƙasashen Waje

Adadin ƴan jaridar da Isra’ila ta kashe a Gaza ya kai 132

Published

on

Isra’ila ta kashe ƙarin ƴan jarida biyu a wani hari da ta kai musu ta sama a tsakiyar Gaza da aka yi wa ƙawanya, lamarin da ya kai adadin ƴan jaridar da ta kashe zuwa 132, in ji hukumomin Falasɗinu.

A wata sanarwa da ofishin watsa labarai na gwamnatin Falasɗinu da ke Gaza ya fitar, ya ce daga ranar 7 ga watan Oktoba da Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare zuwa yanzu, ta kashe ƴan jarida 132, idan aka haɗa da Mohammad Yaghi da Musab Abu Zaid waɗanda jiragen yaƙinta suka kashe ranar Juma’a.

Isra’ila ta kashe ƴan jaridar biyu tare da iyalansu a hari ta sama da ta kai sansanin ƴan gudun hijira na Nuseirat, a cewar hukumomin Falasɗinu.

Dakarun Isra’ila sun ƙaddamar da hare-hare ta sama da ta ƙasa da kuma ta ruwa ne a Gaza ranar 7 ga watan Oktoba bayan ƙungiyar Hamas ta kai harin ba-zata a Isra’ila sakamakon musgunawar da take yi wa Falasɗinawa da keta haddinsu da mamayar da ta yi wa Masallacin Ƙudus.

KU KUMA KARANTA: Yaran Gaza sun yi zanga-zangar adawa da mamayar Isra’ila ta hana su abinci da ruwa

Hare-haren da Isra’ila ke kai wa Gaza sun yi sanadin mutuwar Falasɗinawa aƙalla 29,514, galibinsu mata da ƙananan yara, tare da jikkata fiye da mutum 69,616.

Yaƙin da Isra’ila ta ƙaddamar a Gaza ya raba fiye da kashi 85 na mazauna yankin da muhallansu inda suke fama da ƙarancin abinci da ruwa mai tsafta da magunguna, yayin da yaƙin ya lalata kashi 60 na gine-ginen yankin, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya.

A karon farko tun da aka ƙirƙiri ƙasar Isra’ila a 1948, an gurfanar da ita a gaban kotun ƙasa da ƙasa bisa zargin kisan kiyashi a Gaza.

A watan Janairu, kotun ta bai wa Isra’ila umarni ta daina kisan kiyashi sannan ta bari a kai wa fararen-hular Gaza kayan jinƙai ba tare da shamaki ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like