Connect with us

Labarai

Abin da ya sa muka dakatar da Alƙalan kotunan Majistiri 3 – Hukumar kula da shari’a ta jihar Kano

Published

on

Abin da ya sa muka dakatar da Alƙalan kotunan Majistiri 3 - Hukumar kula da shari'a ta jihar Kano

Abin da ya sa muka dakatar da Alƙalan kotunan Majistiri 3 – Hukumar kula da shari’a ta jihar Kano

Daga Idris Umar, Zariya

Hukumar kula da harkokin Shari’a ta Jihar Kano (JSC) ta dakatar da Alƙalan Kotun Majistare uku saboda samun su da laifi a yayin gudanar da ayyukansu.

Kakakin kotunan jihar Kano, Baba Jibo Ibrahim, ya sanar cewa an dakatar da alƙalai uku daga ayyukan shari’a, yayin da aka bayar da takardar gargaɗi ga magatakardar kotu guda ɗaya.

Alƙalan da aka dakatar sun haɗa da Talatu Makama ta kotun Majistare Mai lamba 29, da Babbar Majistire Rabi Abduƙadir ta Kotun Majistire mai lamba 48 da Alƙalin kotun Majistire mai lamba 60, Tijjani Saleh Minjibir.

Na huɗunsu shi ne Magatakarda Abdu Nasir da ke sashin ɗaukaka ƙara da ke Babbar Kotun Jihar Kano.

Sanarwar ta bayyana cewa kwamitin karɓar korafe-korafen jama’a na ɓangaren shari’ar ya samu Alƙali Talatu Makama da laifin rashin ɗa’a inda ta bayar da umarni ga Bankin GT ya tura kuɗi zuwa asusun mai shigar da ƙara bayan ta san cewa asusun a rufe yake, inda daga ƙarshe aka sanya kuɗin cikin asusunta.

Haka kuma Hukumar ta same ta da laifin nuna rashin ƙwarewa inda taje karɓar shari’a tare da bayar da oda ga ’yan sanda tun kafin shari’ar ta zo gabanta.

KU KUMA KARANTA: Kotu ta ƙwace dala milyan 4 da dubu 700 da naira miliyan 830 da sauran kadarori daga hannun Emefiele

“Saboda haka an sauke Babbar Alƙali Talatu Makama daga kujerarta an kuma dakatar da ita daga dukkan ayyukan shari’a nan take.

“Sai dai wannan bai shafi kasancewarta ma’aikaciyar gwamnati ba,” in ji sanarwar.

Takarda ta ci gaba da cewa, bayan binciken Hukumar ta JSC kan dambarwar shari’ar da ke tsakanin ƙwamishinan ’yansanda da wani Abubakar Salisu da ke gaban Alƙalin Kotun Majistare Mai lamba 48 Rabi Abduƙadir, an same ta da laifin yin sakaci a shari’a.

“Don haka hukumar ta dakatar da ita daga aikin shari’a na tsawon shekara guda.

“Sannan an umurce ta da ta daina duk wani aiki a Kotun Majistare mai lamba 48.”

Hukumar ta kuma dakatar da Alƙalin Kotun Majistire mai lamba 60 Tijjani Saleh Minjibir na tsawon shekara 1 bisa samun sa da laifin rashin ɗa’a.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Published

on

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

Ƙaramar Hukumar Kwami ta kafa kwamitin tsaro saboda rikicin manoma

A ƙoƙarinsa na kauce wa rikicin manoma da makiyaya da ke yawan faruwa a lokacin damuna, Shugaban Karamar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, Dakta Ahmed Wali Doho, ya kafa kwamitin tsaro da sanya ido kan ɓangarorin.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke garin Malam Sidi, shugaban karamar hukumar, ya bukaci manoma da su guji noma burtalolin shanu, wanda hakan ke haifar da rikici tsakaninsu da makiyaya, da ke haifar da asarar rayuka.

Su ma makiyayan ya gargade su da cewa su guji shiga gonakin manoma, saboda hakan ne ke jawo rikici idan suka cinye musu amfanin gona.

A cewarsa, lokacin girbi me aka fi samun rikicin manoma da makiyayan, saboda haka kwamitin zai ci gaba da sa ido daga yanzu har zuwa lokacin girbin don ganin ba a samu rikici ba.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Yusuf ya amince da sayen taki na naira biliyan 5 don manoman Kano

Ya ƙara da cewa, kusancin garin Kwami da rafi ya sa ya zama wuri mai kyau don noman rani.

Don haka ya ja hankalin manoman yankin da su yi amfani da wannan damar wajen bunkasa tattalin arzikinsu.

Ya jaddada cewa noman rani na da matukar muhimmanci wajen magance matsalar karancin abinci a Najeriya.

Hakan ne ya sa suka haɗa kan matasan yankin don su fara noman rogo da zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin abinci da rage wa manoma tsadar takin zamani.

Continue Reading

Labarai

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Published

on

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da ɓata-garin cikin

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin yin gyara da kuma tantance ’yan banga domin kawar da bata-gari a cikinsu.

Kwamishin ’yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya sanar da shirin bayan an kama wasu ’yan banga uku da aikata manyan laifuka.

Ya jaddada muhimmancin sake duba ayyukan ’yan banga a jihar, duk da  muhimmiyar rawar da suke takawa wajen taimaka wa jami’an tsaro a yaki da miyagun laifuka.

Ya ce yin gyaran da kuma tantancewa ya zama dole sakamakon ƙorafe-ƙorafen neman yin hakan daga jama’a.

Ya bayyana cewa jama’a sun yi ƙiran ne bayan kama wasu ’yan banga uku da laifin hada baki wajen shiga gida, sata, ƙwace da kuma sayar da kayan sata a Damaturu.

Wata sanarwa da DSP Dungus Abdul Karim, kakakin rundunar, ya fitar, ta ce wasu daga cikin ’yan banga sun kai korafi bayan faruwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 a Kaduna, sun kai hari a ofishin ƴan sanda a Zamfara

“A ranar 27 ga watan Yuni, 2024, rundunar ta amsa kiran wani mai shago a Damaturu, wanda ya dauki ’yan banga aikin gadi, amma suka kwashe kayan shagon na makudan kudade ba tare da bayani ba.

“Bincike ya kai ga kama wasu mutane biyu da kayan sata da ake zargin sun saya ne daga wani dan banga wanda nan take aka kama shi.

“Ana shawarta jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen daukar masu gadi, sannan su kai rahoton ’yan banga da aka ga suna aikata laifi a bakin aikinsu.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, rundunar tana ɓullo da tsare-tsare don daukar bayanan ’yan banga domin sa ido kan ayyukansu.

Ta ci gaba da cewa ofisoshin ’yan sanda na yankuna da ke jihar za su jagoranci wannan aikin tantancewan domin kawar da baragurbi a cikin ’yan banga.

“Don  haka ake ƙira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda wajen jainrahoton ayyukan jami’an tsaron da ba su dace ba a hedkwatar jihar ta lamba 07068858500, ko kuma a gabatar da wasikar korafin ga kwamishinan ’yan sanda  ta hanyar kakakin rundunar,” in ji sanarwar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like