Connect with us

Labarai

A gudanar da cikakken bincike kan harin da aka kai wa ‘yan sanda a Abuja – Sufeto Janar

Published

on

Sufeto-Janar na ‘yan sanda, IGP, Olukayode Egbetokun ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan harin da aka kai wa wani jami’in ‘yan sanda, Insp. Omeje Matthew a Abuja.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja.

Ya ce I-G ya ba da wannan umarni ne a lokacin da ya ziyarci jami’in da ke jinya a asibitin ƙasa da ke Abuja.

Mista Egbetokun ya ce sun kai ziyarar ne domin duba halin da jami’in da wasu ‘yan bindiga suka kai masa a gidansa da ke unguwar Kabusa a birnin tarayya Abuja.

Ya umarci kwamishinan ‘yan sanda (CP) mai kula da babban birnin tarayya Abuja da ya gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe sojojin Nijar a yankin Tillabery

A cewarsa, binciken shi ne don tabbatar da cewa an gaggauta cafke waɗanda suka aikata laifin tare da gurfanar da su a gaban ƙuliya.

IG ya kuma buƙaci sauran kwamishinonin ‘yan sanda da kwamandojin Dabarun da su tabbatar da rufe duk wani bincike da ake yi kan hare-haren da ake kai wa jami’an ‘yan sanda da a yankunansu.

“Harin da aka kai wa jami’in ‘yan sanda da ke bakin aiki ko kuma ba ya aiki, hari ne ga ɗaukacin jami’an tsaro da zaman lafiya da tsaron al’ummarmu,” in ji shi.

Ya nuna rashin gamsuwa da hare-haren da ake kai wa jami’an ‘yan sanda, ya kuma yi gargadɗin cewa ba za a amince da irin waɗannan hare-haren ba.

Shugaban ‘yan sandan ya yi addu’ar Allah ya ba sufeton ‘yan sandan da sauran waɗanda ke cikin wannan hali lafiya.

Ya kuma yi alƙawarin ɗaukar nauyin rundunar ‘yan sandan Nijeriya na tallafa wa da kuma taimaka wa iyalan jami’an da abin ya shafa.

Mista Egbetokun ya buƙaci jama’a da su bai wa ‘yan sanda haɗin kai wajen bayar da bayanan da ka iya kawo ƙarshen hare-haren da ake kaiwa jami’an ‘yan sanda.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like