No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sojoji sun nemi goyon bayan ƴan Najeriya wajen yaƙar ta’addanci

Rundunar Sojin Najeriya ta bukaci tallafin ‘yan kasa domin samun nasarar murkushe ‘yan ta’adda da sauran barazanar tsaro.

Babban hafsan Sojan ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayyana hakan a Taron alaka Tsakanin Sojoji da Fararen Hula na na ƙarshen shekarar 2025, a Jos, Jihar Filato.

Shaibu ya jaddada muhimmancin kafafen yada labarai wajen bayar da rahotanni na gaskiya da daidaito kan ayyukan rundunar soji, da kuma gujewa yada labaran karya da suka shafi tsaro.

KU KUMA KARANTA: Dole sojojin Najeriya su koyi harsunan gida don samun sahihan bayanan sirri — COAS

Ya kara da cewa, duk wani bayani da zai iya janyo rikice-rikice ko barazana ga kasa ya kamata a tabbatar da sahihancinsa kafin a yada shi, musamman bayanan da ake samarwa ta fasahar AI.

Babban Kwamandan Alaka Tsakanin Sojoji da Fararen Hula, Manjo Janar Musa Etsu-Ndagi, ya ce rundunar za ta ci gaba da samar da sahihan bayanai ga kafafen yada labarai domin inganta fahimtar juna da hadin kai a tsakanin sojoji da jama’a.

Taron ya mayar da hankali kan yadda rundunar soji da kafafen yada labarai za su hada kai wajen magance kalubalen tsaro da kuma tabbatar da zaman lafiya a kasa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...