No menu items!

Sample Page Title

Date:

Majalisar dokokin Najeriya ta amince shugaba Tinubu ya sake ciyo bashi

Majalisar dokokin Najeriya ta amince da bukatar shugaban ƙasa, Bola Tinubu, na karɓo bashin dala biliyan 2.347 daga kasuwannin hada-haɗar kuɗi ta duniya domin cike giɓin kasafin kuɗin 2025 da kuma sake biyan takardun lamuni na Eurobonds da ke ƙarewa.

Tinubu ya bayyana cewa bashin zai kasance bisa tanade-tanaden dokar kula da bashi ta 2003, wadda ke buƙatar amincewar majalisa kafin ɗaukar sabon bashi ko sake biyan tsoffin bashi.

KU KUMA KARANTA: Idan ba a yi wasa ba Tinubu zai fara ciyo bashi a Opay da Moniepoint da Palmpay – Dino Melaye

Shugaban ƙasa ya ce za a samo kuɗin ne ta hanyar kayan aikin kuɗi kamar Eurobonds da haɗin bashi daga bankuna, ko wasu hanyoyin wucin gadi dangane da yanayin kasuwa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...