No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ana zargin kwamishina a Kano ya fitar da Naira biliyan 1.17 na kwangilar bogi

Daga Jameel Lawan Yakasai

Kwamishinan raya karkara na Kano, Abdulkadir Abdulsalam, ya shiga zargin badakalar kudi da ake cewa ta kai naira biliyan 6.5, bayan amsarsa kan wati kwangilar bogi da ya sa hannu a kai.

Jaridar Neptune Prime ta tattaro daga jaridar Premium Times cewa Abdulsalam ya amsa fitar da sama da naira biliyan 1.17 a watan Nuwamba 2023, abin da aka bayyana a matsayin tushen badakalar.

Rahoton ya kuma ce an bi ta hannun kamfanoni na bogi da ‘yan canji wajen karkatar da kudin, har ma aka bai wa wasu mutane dala miliyan daya a Abuja.

KU KUMA KARANTA: Na yi murabus ne domin maslahar al’ummar jihar Kano – Kwamishinan Sufuri

Rahoton ya nuna Hukumar ICPC ta riga ta karbo naira biliyan 1.1 daga cikin kudaden, yayin da kotu ta kwace karin naira miliyan 142 daga asusun da ake alakanta da Daraktan Fadar Gwamna Abba Kabir Yusuf, Abdullahi Rogo.

Sai dai wata kotu a Kano ta bayar da umarnin dakatar da ICPC da EFCC daga ci gaba da bincike, lamarin da kungiyoyin farar hula suka soki.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...