No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sai na jawo Tinubu ya yi asarar ƙuri’u sama da miliyan 1 a zaɓen 2027 – Sanata Kabiru Marafa

Tsohon Ɗan Majalisar Dattawan Najeriya mai wakiltar Zamfara ta Tsakiya, Sanata Kabiru Marafa ya sha alwashin rage wa Tinubu ƙuri’u masu yawa a zaɓen 2027.

Marafa, wanda a baya-bayan nan ya sanar wa BBC ficewarsa daga jam’iyyar APC, bayan ya zargi Tinubu da ”watsar da shi bayan cin zaɓe” ya ce sai ya kawo wa shugaban ƙasar cikas a zɓen 2027 da ke tafe.

KU KUMA KARANTA: A lissafin da na yi, Tinubu na uku zai zo a zaɓen shugaban ƙasa na 2027 – El-Rufai

Yayin wata hira da hgidan talbijin na Channels, Sanata Marafa ya ce sai ya janyo wa Tinubu asarar kimamin ƙuria’ miliyan guda.

Tsohon ɗan majalisar – wanda ya kasance babban daraktan yaƙin neman zaɓen Tinubu a Zamfara a 2027 – ya ce zai nuna wa shugaban ƙasar matsayinsa a siyasar jihar Zamfara.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...