No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar NSCDC ta kama mutane 6 da ake zargi da lalata wutar Lantarki a Jihar Kano

Daga Jameel Lawan Yakasai

Hukumar Tsaro ta Civil Defence (NSCDC) a Jihar Kano ta kama mutane shida da ake zargi da sata da lalata kayan wutar lantarki a unguwar Hayin Da’e da Hotoro da ke yankin ƙaramar hukumar Tarauni.

Sanarwar da kakakin hukumar a kano SC Ibrahim Idris Abdullahi ya fitar a ranar Talata, 2 ga Satumba, 2025.

Sanarwar ta ce an kama mutanen ne bayan samun bayanan sirri daga yan sa kai a yankin, inda aka cafke su da wayoyin lantarki da suka cire daga kan wata transformer cikin dare.

KU KUMA KARANTA: Hukumar NSCDC ta kama mutane 7 da ake zargi da sace murafan kwalbati

Daga cikin waɗanda aka kama akwai Muhammad Yusuf mai shekara 18, Muhd Sani Adamu 19, Umar Musa 19, Ahmed Auwal 20, Muhd Yusuf 28 da kuma Usman Ali 19, waɗanda yawancinsu mazauna yankin ne.

NSCDC ta bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa waɗannan mutane sun dade suna addabar al’ummar Hayin Da’e, Farawa Kwanar Yashi da Hotoro ta hanyar fasa ƙofa, sata da kuma lalata kayan wutar lantarki.

Hukumar ta ce ta fara cikakken bincike, inda za a mika wadanda ake zargin kotu bayan kammala rahoto.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...