No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumomi a Kano sun amince da mafi ƙarancin sadakin aure Naira dubu 20

Daga Jameel Lawan Yakasai

Hukumar zakka da hubusi ta jihar Kano tare da hukumar shari’a da majalisar malamai da ƙungiyar limaman masallatan Juma’a da ƙungiyar ma’aikatan zakka da waƙafi ta ƙasa sun amince da sabbin ka’idoji kan nisabin zakka, diyyar rai dasadakin Aure a jihar.

A taron da aka gudanar a Kano ranar Alhamis, an yanke shawarar amincewa da Naira dubu 20 a matsayin mafi ƙarancin sadakin aure, Naira miliyan 150 a matsayin diyya ga wanda aka kashe bisa kuskure da kuma naira dubu 985 a matsayin nisabin zakka, bisa lissafin farashin Durham.

KU KUMA KARANTA: Hukumar zakka da waƙafi ta raba kayayyakin jin ƙai ga marasa galihu a Zamfara

Babban sakataren ƙungiyar ma’aikatan zakka da wakafi ta kasa, Farfesa Aliyu Dahiru Muhammad na jami’ar Bayero Kano ne ya bayyana cewa taron ya kuma amince a ci gaba da gudanar da irin wannan zama duk bayan wata uku domin dubawa da sabunta wadannan ka’idoji.

Haka kuma, an tsara a sanar da gwamnatin jihar domin shirya taron wayar da kai tare da ƴan jarida da kuma isar da sakonni ta hanyoyin da suka dace.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...