No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin tarayya ta dakatar da samar da sabbin jami’o’i a ƙasar

Daga Jameel Lawan Yakasai

Majalisar zartarwa ta ƙasa, karkashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a ranar Laraba ta amince da dakatar da kafa sababbin makarantun gaba da sakandire na tarayya a duk faɗin ƙasar na tsawon shekaru biyar.

Dakatarwar ta shafi jami’o’i, kwalejojin kimiyya da fasaha (polytechnics), da kuma kwalejojin ilimi.

Ministan Ilimi, Tunji Alausa ne ya bayyana hakan a yayin zaman majalisar.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya canza sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari

Alausa ya bada dalilan wannan mataki da cewa babban ƙalubale a fannin ilimi a Najeriya yanzu ba samun damar shiga makarantu ba ne, illa magance yawaitar kafa sababbin makarantun da dama can akwai su.

A cewar sa, hakan ya janyo tabarbarewar ilimi ta hanyar ƙarancin gine-gine da ma’aikata.

“Idan ba mu ɗauki mataki da gaggawa ba, to ilimin gaba da sakandire zai ci gaba da lalacewa kuma kimar ɗaliban Nijeriya za ta zube a idon duniya,” in ji Ministan.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...