An ɗaura auren jaruma Rahma Sadau a Kaduna
Daga Shafaatu Dauda Kano
Fitacciyar juruma a masana’antar Kannywood, Rahama Sadau an ɗaura mata aure tare da Angonta Alhaji Ibrahim Garba a yau Asabar 9 ga Watan Agusta na shekarar 2025 a jihar kaduna.
An ɗaura auren nata a kan sadaki Naira 300,000 da misalin ƙarfe 11:00 na safe a masallacin Atiku Auwal dake Unguwar Rimi.
KU KUMA KARANTA: Hisbah a Kano, ta kama wasu masoya biyu da suka ɗaura aure a gidan cin abinci
Auren ya samu halartar ‘yan’uwa da abokan arziki da dama, daga ciki da wajen Kaduna.






