No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaba Tinubu zai samar da layin dogo don rage cunkosun ababen hawa a Kano

Daga Jameel Lawan Yakasai

Gwamnatin Tarayya na shirin samar da titin jirgin ƙasa wanda zai riƙa zirga-zirga a cikin birnin Kano don rage cunkoson ababen hawa.

Hon. Abubakar Kabir Abubakar, Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Kasafin Kuɗi ne ya bayyana haka inda ya ce aikin zai ci kimanin Naira tiriliyan ɗaya da rabi.

KU KUMA KARANTA: Najeriya ta karɓo rancen dala biliyan 1.3 don kammala layin dogon Kano zuwa Maraɗi

An shirya wannan aikin ne domin rage cunkoson ababen hawa da kuma samar da wadata ga tattalin arziƙi jihar da zarar an kammala shi.

Hon. Bichi ya kuma bayyana cewa akwai wasu ayyuka da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya fara a Arewacin Najeriya, waɗanda suka haɗa da gyaran ababen more rayuwa, kiwon lafiya, noma, ilimi, da tsaro.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...