Gwamnan Katsina ya tsallake rijiya da baya a wani hatsarin mota da ya rutsa da shi a hanyar Daura zuwa Katsina

0
233
Gwamna Radda ya tsallake rijiya da baya a wani karamin hatsarin mota da ya rutsa da shi a hanyar Daura zuwa Katsina By Ibraheem El-Tafseer Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi wani dan karamin hatsarin mota a yammacin ranar 20 ga watan Yuli, 2025, a lokacin da yake tafiya kan hanyar Daura zuwa Katsina a wani bangare na aikinsa. A cewar wata sanarwa da babban sakataren yada labarai, Ibrahim Kaula Mohammed ya fitar, gwamnan bai samu munanan raunuka ba kuma yana cikin koshin lafiya da kwanciyar hankali. Sanarwar ta kara da cewa Gwamna Radda ya ci gaba da kasancewa cikin farin ciki kuma ya nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki da ya ba shi kariya. Ya kuma mika godiyarsa ga al’ummar jihar Katsina da masu hannu da shuni bisa addu’o’i da kuma damuwarsu. Lamarin dai bai haifar da cikas ba, kuma ana sa ran Gwamnan zai ci gaba da gudanar da ayyukan sa.
Gwamna Dikko Raɗɗa

Gwamnan Katsina ya tsallake rijiya da baya a wani hatsarin mota da ya rutsa da shi a hanyar Daura zuwa Katsina

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi wani ɗan karamin hatsarin mota a yammacin ranar 20 ga watan Yuli, 2025, a lokacin da yake tafiya kan hanyar Daura zuwa Katsina a wani ɓangare na gudanar da aikinsa.

A cewar wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labarai na Gwamnan ya fitar, Ibrahim Kaula Mohammed, gwamnan bai samu munanan raunuka ba kuma yana cikin ƙoshin lafiya da kwanciyar hankali.

KU KUMA KARANTA: Za a gina birnin Dawakai ma fi girma na farko a Katsina

Sanarwar ta ƙara da cewa Gwamna Radda ya ci gaba da kasancewa cikin farin ciki kuma ya nuna godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki da ya ba shi kariya. Ya kuma miƙa godiyarsa ga al’ummar jihar Katsina da duk waɗanda suka yi  addu’o’i da kuma nuna damuwarsu.

Lamarin dai bai yi muni ba, kuma ana sa ran Gwamnan zai ci gaba da gudanar da ayyukan sa.

Leave a Reply