An ɗauko gawar Buhari daga Landan zuwa Najeriya 

0
234
An ɗakuko gawar Buhari daga Landan zuwa Najeriya 
Jirgin da ya ɗauko gawar Muhammadu Buhari

An ɗauko gawar Buhari daga Landan zuwa Najeriya

Gawar tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta baro birnin London, Birtaniya, da safiyar Yau Talata, zuwa garin Daura a Jihar Katsina, domin gudanar da jana’izar sa.

Jaridar PUNCH Online ta ruwaito cewa an dauko gawar tsohon shugaban kasar ne a jirgin saman Najeriya.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ke jagorantar tawagar gwamnatin tarayya da shirye-shiryen dawo da gawar tsohon shugaban kasar zuwa gida.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Yobe ta ayyana gobe Talata a matsayin ranar hutu, don juyayin mutuwar Buhari

A jiya Litinin, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu zai karɓi gawar tsohon shugaban kasar a Katsina kafin a kai ta Daura don binne wa.

Ministan Watsa Labarai da Tsare-Tsaren Ƙasa, Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar a birnin Abuja.

Leave a Reply