No menu items!

Sample Page Title

Date:

An kubutar da Ƴan Najeriya 13 da akayi Safararsu zuwa kasashen ketare

Daga Shafaatu Dauda Kano

Hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje (NIDCOM), ta karɓi wasu ƴan ƙasar 13 da akayi safararsu zuwa ƙasashen Ghana da Mali.

Shugabar hukumar, Abike Dabiri-Erewa, ce ta sanar da hakan a yayin da take tarbar waɗanda abin ya shafa da suka haɗa da ƴan mata 12 da yaro 1 ɗan shekara biyar, a cewar sashen Hausa na BBC.

KU KUMA KARANTA:An ƙaddamar da shiri kan take haƙƙin yara a Najeriya

Ƴan matan da aka ceto sun ce an yi musu wayo ne tare da tilasta musu shiga karuwanci, bayan an yaudare su da cewa za a samo musu aiki a Ghana da Mali, baya ga cin zarafin su da wadanda suka yi safarar tasu suka yi.

Matsalar safarar al’umma ta hanyar yaudarar su da cewa za a samo musu aiki a ƙasashen waje ya daɗe yana addabar ƙasar, inda ko a ƴan watannin baya an sami nasarar dawo da wasu matasa daga Ghana waɗanda aka tilastawa yin laifuka ta intanet.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...