No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar Hisbah a Kano ta kama matasan da ba sa yin azumi da masu aikin banza

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Jami’an Hukumar Hisba a jihar Kano sun kama wasu matasa gandaye da ake zargi da kin yin azumi a ranar farko ta watan Ramadan.

Mataimakin babban kwamandan hukumar, Dakta Mujahideen Aminuddeen ne ya tabbatar da kamen ga manema labarai a jihar.

Ya kara da cewa an kama matasan ne yayin sintiri da jami’an hukumar ke yi a sassa daban-daban na birnin Kano.

Haka kuma, hukumar ta cafke kimanin mutane 60 da ke da askin banza, wanda ya sabawa dokokin shari’a da al’adun gari.

Bugu da kari, Hisba ta kama wasu direbobin baburan adaidaita sahu (keke napep) da ake zargi da cakuda maza da mata a baburansu, lamarin da hukumar tace ba za ta lamunta da shi ba.

Hukumar ta Hisba ta bayyana cewa za ta ci gaba da gudanar da sintiri don tabbatar da bin dokokin shari’a a cikin watan Ramadan.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...