No menu items!

Sample Page Title

Date:

Indai sahihin zaɓe za a yi NNPP za ta kayar da APC da PDP – Kwankwaso

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Sanata Rabiu Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya ce jam’iyyar NNPP za ta kayar da dukkan jam’iyyun siyasa a zaɓe mai inganci da adalci.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) na jam’iyyar a Abuja.

Dan takarar NNPP a zaben 2023 din ya soki gwamnatin Bola Tinubu, yana mai cewa ‘yan Najeriya na fuskantar matsin rayuwa fiye da yadda aka taba gani a baya.

KU KUMA KARANTA:Kotu ta aikewa Abdullahi Abbas da Faizu Alfindiki sammaci bisa zargin ɓatanci ga gwamnan Kano

“Gaskiya ne da wuya a tuna da wani da ke farin ciki da gwamnatin APC a kowane mataki, musamman a matakin tarayya,” in ji shi.

“‘Yan Najeriya sun shaida wahalhalu da ba a taba gani ba a tarihin wannan kasa.

“Talauci ya yadu ko’ina. Mun ga rashin tsaro, gine-gine da ababen more rayuwa suna lalacewa, kuma ba mu ga wani kokari na gyara su ba.

“Na yi imani idan aka gudanar da sahihin zabe a wannan kasa, jam’iyyarmu za ta kayar da APC, PDP da sauran jam’iyyu.”

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...