No menu items!

Sample Page Title

Date:

Za mu yiwa filin jirgin saman Legas ginin zamani – Ganduje

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Shugaban kwamitin Daraktoci na Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama na Ƙasa (FAAN), Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya jaddada bukatar gyara na gaggawa a filin sauka da tashi na jirgin sama dake Murtala Muhammed (MMIA) a cewar sa, ya fara zama tsohon yayi.

KU KUMA KARANTA:Kotu ta da ɗage sauraron ƙarar Abdullahi Ganduje kan zargin badaƙalar kuɗaɗe

Yayin ziyarar gani-da-ido ta farko da ya kai MMIA, tare da rakiyar Manajan Daraktan FAAN, Misis Olubunmi Kuku, Ganduje ya tabbatar da cewa yawancin kayan aikin filin jirgin saman sun tsofa wasu kuma sun lalace.

Ya kuma bai wa masu ruwa da tsaki tabbacin cewa kwamitin zai hada kai da hukumar ta FAAN domin gyara filin jirgin da zamanantar da shi, wanda zai yi daidai da yadda filayen jiragen sama su ke a faɗin duniya.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...