No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban ’yansandan Mopol na Legas ya Musulunta a Kano

Daga Jamilu Lawan Yakasai

Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda da ya yi fice wajen kwatanta gaskiya da amana, ACP Daniel Amah, ya karɓi Addinin Musulunci a Fadar Sarkin Kano.

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ne, ya jagoranci musuluntar da shi tare da sanya masa sabon suna, Muhammadu Sanusi.

Sarkin ya yi ƙira ga Muhammad Sanusi da ya zurfafa iliminsa na addinin Musulunci, ciki har da koyon yadda ake sallah, azumi, da bayar da zakkah.

Haka kuma, ya shawarce shi da ya ci gaba da girmama iyayensa, duk da bambancin addininsu, tare da riƙe kyawawan halayensa.

Sunan Mista Amah, ya yi amo a watan Afrilun 2022 bayan ya ƙi karɓar cin hancin dalar Amurka 200,000 da wasu ’yan fashi suka ba shi.

‘Yan fashin sun sato kuɗi sama da Naira miliyan 300, amma daga bisani suka shiga komarsa.

KU KUMA KARANTA: Yan sanda sun kama wani da ya caka wa ’yar shekara 8 almakashi a gabanta

Wannan hali nasa na riƙon gaskiya ya sa aka ɗaga darajarsa zuwa Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda a watan Nuwamban 2022.

Da yake magana kan dalilin da ya sa ya karɓi Addinin Musulunci, Muhammad Sanusi ya bayyana godiyarsa bisa kyakkyawar tarba da ya samu kuma ya yi alƙawarin neman ilimin addini tare da ci gaba da yi wa al’umma hidima.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...