No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar NAFDAC ta rufe babban kantin ‘yan China

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC), ta rufe wani babban kanti na ‘yan China da ke unguwar Wuse 2 a Abuja, bisa zargin sayar da kaya masu tambari da harshen China ba tare da izinin hukumar ba.

Daraktan bincike na NAFDAC, Shaba Mohammed ne, ya bayyana wa manema labarai cewa galibin kayan da ake sayarwa a kantin sun ƙunshi tambari da rubutu cikin harshen China, wanda ya saɓa wa dokokin ƙasa.

“Za mu binciki sama da kashi 90 na kayan da ke cikin wannan kantin don gano yadda aka shigo da su cikin ƙasar nan,” in ji Shaba Mohammed.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta rufe wani kamfani a Legas mai samar da jabun kayan kwalliya

Ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin kayan da ake sayarwa a kantin sun ƙare wa’adin amfaninsu, amma har yanzu ana ci gaba da sayar wa jama’a.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...