No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yansanda a Kano sun kama mutum 3 da jabun kuɗi

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama wasu mutum uku da aka samu da jabun kuɗi har Naira biliyan 129.

Kakakin rundunar, SP Haruna Kiyawa ne, ya bayyana wa manema labarai a Kano ranar Talata cewa jabun kuɗin sun haɗa da Dalar Amurka, CFA da Naira.

Ya ce adadin kuɗin da aka ƙwato sun haɗa da dala 3,366,000, CFA51,970,000, da Naira 1,443,000.

SP Kiyawa, ya ƙara da cewa waɗanda ake zargin, suna hannun ‘yan sanda kuma suna taimakawa wajen bincike don gano inda ake buga jabun kuɗin.

KU KUMA KARANTA: An kama malaman bogi a jami’ar Bayero da ke Kano

Baya ga kuɗin, ’yan sanda sun kuma ƙwato harsasai guda shida, Adaidaita Sahu guda uku, babura guda takwas da kuma jakunkuna uku ɗauke da tabar wiwi.

Sauran kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da ƙwayoyi 250 na diazepam, tumaki 278, da shanu guda bakwai.

Kiyawa, ya ce kama waɗannan mutane na nuna yadda rundunar ke ƙoƙarin yaƙi da laifuka a Kano.

Ya ƙara da cewa rundunar ta magance manyan laifuka kamar garkuwa da mutane, fashi da makami, safarar miyagun ƙwayoyi, da kuma rikicin daba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...