No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu karnuka sun kashe wani mai gadi

Ana zargin karnuka sun kashe wani jami’in tsaron gidaje a yankin Lekki a Jihar Legas, bayan da karnukan suka tsere daga gidan mai su.

Wani bidiyo da @itzbasito ya wallafa a X, an ga karnukan suna yawo a kusa da gawar mutumin da ke kwance a kasa.

Ya wallafa a jikin bidiyon cewa, “Jiya da dare a Pinnock Estate wani mai gida bai kulle karnukansa yadda ya kamata ba, inda suka tsere suka kashe wani mai tsaron Estate ɗin har lahira,” in ji shi.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sanda a jihar Legas, SP Benjamin Hundeyin, ya ce, “An kama mai karnukan kuma yana hannunmu.”

Masu amfani da kafofin sada zumunta sun bayyana damuwa kan kashe jami’in tsaron yayin da wasu ke neman a yi adalci, wasu kuma suke zargin cewa an yi rufa-rufa ne.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar mai gadi rataye a wata makarantar firamare a Gombe

A cewar Redrum-MUFC, “Karnuka ba su yi haka, wannan dai akwai rufa-rufa. Galibi idan karnuka suka yi kisa irin wannan, ba sa barin gawar sai sun yaga jikinta.

“Jama’a muna ganin jini a kasa, amma babu tabon jini a jikin karnukan,” in ji shi.

Amma Oluwamooregrin ya nuna shakku kan alamar shigar karnuka a cikin ayyukan.

“Ba na jin boerboels za su iya yin haka sai idan an horar da su da cin danyen nama, labarin bai cika ba kuma yaya girman rukunin gidajen yake, har ba a lura da gudu da ihun mamacin ba?,” in ji shi.

Sai dai Clover Lavender ya jaddada cewa ya kamata mai karnukan ya fuskanci fushin doka.

“Dole ne a ɗaure mai karnukan kuma a kulle shi har abada,” in ji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...