No menu items!

Sample Page Title

Date:

An gano baraguzan jirgin da ya faɗa ruwa a Fatakwal

Hukumar bincike da kiyaye haɗurra ta Najeriya (NSIB) ta ce an gano baraguzan jirgin sama mai sauƙar ungulu da ya faɗi a teku a Fatakwal da ke jihar Ribas.

A ranar 24 ga watan Oktoba, jirgin ɗauke da mutum takwas, fasjinja shida da matuƙa biyu ya faɗi a yankin ruwan Bonny Finima.

KU KUMA KARANTA:Wani jirgi da NNPCL ya ɗauka ya yi hatsari a Fatakwal

Tuni dai an gano gawarwakin mutum biyar da aka tsamo daga ruwa. Kamfanin man fetur na NNPCL a Najeriya ya ce shi ne ya dauki shatar jirgin.

Cikin wata sanarwa da ta fitar, Darektar yada labarai da tallafawa iyali a hukumar ta NSIB Mrs. Bimbo Oladeji ta ce an gano jirgin ne a zurfin ruwan da ya kai mita 42 a cewar jaridun Najeriya

Rahotanni sun ce gwanayen ninƙaya ne suka gano baraguzan jirgin.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...