No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙungiyar NASU da SSANU sun tsunduma yajin aiki

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jami’o’i, sun tsunduma yajin aiki sakamakon rashin biyan su albashi wata huɗu.

Gamayyar ƙungiyoyin (JAC), waɗanda suka haɗa da Ƙungiyar Ma’aikatan Jami’o’i (NASU) da Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’i na Najeriya (SSANU).

A cikin wata sanarwa da ta aike wa dukkanin shugabannin ƙungiyar da ke jami’o’i da su fara yajin aikin a ranar Lahadi.

Sanarwar, wadda Sakataren NASU, Mista Peters Adeyemi da Shugaban SSANU, Mista Mohammed Ibrahim, suka sanya wa hannu, a ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce: “Mun yanke wannan hukunci ne sakamakon dakatar da albashinmu ja wata huɗu.”

KU KUMA KARANTA: JOHESU ta ayyana yajin aikin gargaɗi na kwanaki 7

Duk da cewar Shugaba Bola Tinubu ya amince da biyan kashi 50 na albashin da aka dakatar, amma JAC ta ce babu wanda ya samu ko sisi daka cikinsu.

JAC, ta bayyana cewa ta gargaɗi gwamnati a lokuta daban-daban, amma ba a yi komai kan buƙatarsu ba.

Saboda haka, JAC ta yanke shawarar cewa za a fara yajin aikin ne misalin ƙarfe 12 na daren ranar Lahadi, 27 ga watan Oktoba, 2024.

Ƙungiyar ta ce sai gwamnati ta waiwaye sannan za su janye yajin aikin da za su fara a daren yau.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...