Tsadar Rayuwa: Wani mutum ya kashe kansa

0
45
Tsadar Rayuwa: Wani mutum ya kashe kansa

Tsadar Rayuwa: Wani mutum ya kashe kansa

Daga Idris Umar, Zariya

Wani mutum ya kashe kansa saboda tsadar rayuwa a maraban garin Kaba dake Lokoja jihar Kogi.

Wata mata da ta nemi a sakaya sunanta ta baiyana yadda lamarin ya faru ga jaridar Neptune Hausa ta wayar salula cewa, mamacin ya daɓawa kansa wuƙane a wuya da cikinsa yayin da ya sami wuƙa a wajan wani mai sayar da lemun zaƙi.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe biyu na yammacin jiya litinin 21/10/24 amma kafin ya rasu ya baiyana dalilinsa na yin haka.

Mamacin ya baiyana cewa, shi daga garin Tudun Wadan Ɗan Kade na jihar Kano yake kuma yana da mata da yara 3 a garin nasu amma bai faɗi sunansa ba.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sanda a jihar Yobe sun kama wata mata da kashe mijinta da wuƙa

Mamacin ya ƙara da cewa wahalar rayuwace ta fito dashi domin bashi da wata hanyar da zai rinka ciyar da iyalinsa, yabi duk wata hanyar da zai tsara da rayuwarsa amma lamarin ya faskara bisa haka ya zaɓi ya bar duniya kawai.

Ƙarshe mamacin yace, a sanar da matarsa da yaransa su yafe masa don shi ya tafi kenan bazai dawoba.

Ya gama faɗin haka kenan sai rai yayi halinsa inji majijiyar tamu.

Amma bincike ya tabbatar da cewa bayan rasuwar nasa ne al’ummar musulmi na wannan anguwa sukai mashi salla kamar yadda Shari’a ya tanada.

Leave a Reply