No menu items!

Sample Page Title

Date:

Za a fara amfani da sabuwar manhajar ilimi a watan Janairun 2025 – Ministan Ilimi

Ma’aikatar ilmin ta sanar da da cewar sabuwar manhajar ilimin firamare dana ƙaramar sakandare zasu fara aiki a faɗin Najeriya a watan Janairun 2025.

Ministan Ilmin, Farfesa Tahir Mamman, wanda ya bayyana hakan yayin taron masu ruwa da tsaki akan yadda za’a aiwatar da sabuwar manhajar a abuja, yace za’a fara amfani da sabuwar manhajar ilmin sakandare a watan satumbar 2025.

Farfesa Mamman ya bayyana cewar sabuwar manhajar zata warware matsalolin koyo da koyarwa dana samun aikin yi kasancewar sabon tsarin koyar da sana’o’in da aka kirkiro zai yi matukar tasiri wajen koyawa dalibai sana’o’in zamani.

KU KUMA KARANTA: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Ya ƙara da cewar za’a shafe watanni 3 masu zuwa ana sharar fage, ciki harda horas da malamai akan yadda zasu yi amfani da manhajar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...