No menu items!

Sample Page Title

Date:

Za a fuskanci ɓarkewar kwalara, rashin abinci da tsaro a Maiduguri – MƊD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗi game da yiyuwar ɓarkewar cutar kwalara a sansanonin ‘yan gudun hijira na wucin gadi da aka kafa a Maiduguri, babban birnin Borno sakamakon ambaliyar ruwa da ya mamaye jihar.

Rahoton da ofishin kula da ayyukan bada agaji na Majalisar Dinkin Duniyar ya fitar, yace abubawan da za’a bukata cikin gaggawa sun hada da abinci da tsaro da wurin kwana da kuma tsaftataccen ruwa, inda ya kara da cewar wasu daga cikin hanyoyin samun ruwan sun gurbace, kuma na iya janyo barkewar cututtuka irinsu kwalara.

An ruwaito rahoton na cewa, “buƙatun gaggawa da ake dasu sun hada da abinci da matsuguni da tsaftataccen ruwan sha, saboda wasu daga cikin hanyoyin samun ruwan sun gurbace.

Tsaro na daga cikin muhimman abubuwan damuwa, musamman ga yaran da basa tare da kowa ko suka rabu da danginsu da tsofaffi da masu bukata ta musamman.

KU KUMA KARANTA: Ambaliyar ruwa a Maiduguri ta shafe wasu sassan garin (Bidiyo)

Wuraren da ambaliyar tafi shafa a birnin Maiduguri sun hada da Gwange da Hanyar Bama da Gidan Namun Daji da Gidan Waya da Sakatariyar Jihar da Titin Legas da Fadar Shehun Borno da babbar kasuwar Maiduguri da yankunan Custom da Gamboru da Budum da Asibitin Kwararru da kuma gaba dayan yankin gidan waya.

Mutane da dama sun rasa matsugunansu, sai dai mahukunta, sun shaida cewa wasu sun soma komawa gidajensu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...