No menu items!

Sample Page Title

Date:

Za mu gurfanar da wasu daga cikin ‘yan kasuwar Singa a kotu – Muhyi Magaji

Daga Shafaatu Dauda, Kano

Shugaban hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe da hana cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhyi Magaji Rimin Gado, ya ce zasu gurfanar da wasu daga cikin ‘yan kasuwar Singa a kotu kan zargin yiwa mutane ƙarin fashin kayayyakin masarufi bayan kammala zanga-zangar lumana.

Muhyi, ya bayyana hakane ta cikin shirin barka da hantsi na gidan radiyon Freedom, ya ce hukumar zata gurfanar da wasu daga cikin ‘yan kasuwar Singa ne sakamakon zargin su da yiwa mutane Karin farashin kaya ba bisa doka.

Haka zalika hannu guda kuma ya ce ana gudanar da bincike kan zargin karkatar da aƙalar shinkafar tallafi da gwamnatin tarayya ta baiwa al’ummar Jihar Kano.

KU KUMA KARANTA: An sace biliyan 50 daga asusun gwamnatin Kano – Muhyi Magaji

Ya kuma ce yanzu haka tuni hukumar ta samo oda daga kotu don fara ɗaukar mataki na farko gabanin zuwa gaban alkalin kai tsaye.

Muhyi, ya kuma ƙara da cewa, hukumar za taci gaba da sanya ido don ganin an tabbatar da aiwatar da dai-daiton da aka samar kan ƙarin farashin kayayyakin masarufin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...