No menu items!

Sample Page Title

Date:

Masu zanga-zanga na cigaba da gudana a Abuja da wasu jihohi

Daga Ali Sanni

Masu zanga-zangar ƙuncin rayuwa da rashin gudanar da mulki mai inganci sun cigaba da zanga-zanga a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja, Ibadan, Abeokuta da Akure bayan tsagaitawa sakamakon ɓata-gari da suka shiga suka kawo cikas.

Idan zaku tuna, ɗaya ga watan Agusta ne masu zanga-zanga suka fito a jihohi da dama na ƙasar domin nuna damuwar gamai da tsarda rayuwa da matsin tattalin arziki da rashin shugabanci na gari a Najeriya.

KU KUMA KARANTA:Zanga-Zanga: DSS ta musanta kai samame ofishin NLC

Sai dai wasu ɓata-gari sunyi amfani da wannan damar wajen kawo tashin hankali da sace kayan al’umma wanda hakan ya jawo asarar rayuka da dukiyar al’umma musamman a jahonin Kano da Kaduna inda abun yafi muni.

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen daya gabata na 2023 ƙarƙashin jam’iyyar African Action Congress ( AAC) Omoloye Sowore ne ya wallafa hotunan fitowa da cigaba zanga-zangar tasu a yau ta shafinsa na X.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...