No menu items!

Sample Page Title

Date:

Aƙalla mutum 20 sun mutu a Bayelsa bayan da kwale-kwalensu ya kama da wuta

Aƙalla mutum 20 ne suka mutu sakamakon kama wuta tare da fashewa da wani kwale-kwalen katako da suke ciki ya yi a jihar Bayelsa a ranar Laraba, in ji ‘yan sanda

Kwale-kwalen na ɗauke ne da ‘yan kasuwar da ke kai kaya yankunan da ke gaɓar teku, a cewar mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda ta jihar Bayelsa, Musa Muhammed a ranar Alhamis.

‘Yan kasuwa kan je yankunan da ke gaɓar teku da kuma babban birnin jihar Yenagoa a duk mako.

KU KUMA KARANTA: Hatsarin kwale-kwale ya yi sanadin mutuwar sama da mutum 90 a Mozambik

Aƙalla mutum 200 ne rahotanni suka ce sun mutu sakamakon hatsarin kwale-kwale a Najeriya a bara kawai, inda hukumomi ke cewa ana yawan samun hakan ne saboda lodi mai yawa da rashin kula da jiragen ruwan.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...