No menu items!

Sample Page Title

Date:

Dubban Falasɗinawa sun tsere daga wani yanki a tsakiyar Gaza

Dubban Falasɗinawa sun tsere daga wani yanki a tsakiyar Gaza sakamakon sabbin umarnin ficewa da Isra’ila ta yi, lamarin da ke ƙara ta’azzara halin jinƙai a wani yanki da tuni ya cika da ‘yan gudun hijirar da ke tsere wa farmaki a kudancin ƙasar.

Sojojin Isra’ila, waɗanda a yanzu suka ƙwace kusan ɗaukacin yankunan a cikin kusan watanni 10 na yaƙin, sun shafe makonni da dama suna ƙaddamar da manyan hare-hare a yankunan da a baya suka yi ikirarin “kore mayaƙan Hamas.”

A harin na baya-bayan nan da ta kai, Isra’ila ta umarci mazauna garin a ranar Lahadi da su ƙaurace wa Al-Bureij da ke arewa maso gabashin Deir.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila tana shirin kai farmaki a wani sansanin ‘yan gudun hijira a Gaza

“Me ya saura? Deir? Deir cike take da mutane, kowa yana Deir, duk Gaza. Ina mutane za su tafi?” Aya Mansour ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters a Deir bayan ta gudu daga Bureij.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...