No menu items!

Sample Page Title

Date:

Za mu kare masu zanga-zanga in dai ta lumana ce – IGP

Babban sufeton ‘yansadan Najeriya, IGP, ya ce sun shirya tsaf domin tunkarar zanga-zangar da wasu ‘yan ƙasar ke shiryawa a wata mai zuwa, yana mai cewa “za mu kare masu zanga-zanga matuƙar dai ta lumana ce”.

Sai dai da yake magana bayan ganawa da manyan jami’an rundunar, Kayode Egbetokun ya yi ƙira ga matasa da su haƙura da zanga-zangar “saboda gwamnati na bakin ƙoƙarinta”.

“Idan zanga-zangar ta lumana ce za ku ganmu muna kare masu zanga-zangar.

Ba mu adawa da zanga-zangar lumana, za mu taimaka wa masu zanga-zangar lumana saboda ‘yancinsu ne” in ji shi lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai.

“Amma kuma akwai alhaki a kanmu na kare rayuka da dukiyoyi.

Ba za mu zauna muna kallon ‘yandaba suna ƙona gine-gine da sunan zanga-zanga ba, ba za mu yarda da wannan ba.”

Ya ƙara da cewa sun samu bayanan yadda wasu ke jiran matasa su kwaikwayi irin zanga-zangar da mutanen Kenya suka yi “kwabo da kwabo” a Najeriya.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya roƙi ‘yan Najeriya da su dakatar da shirin zanga-zanga

“Ina amfani da wannan damar na yi ƙira ga matasan Najeriya, don Allah ku yi watsi da ƙiran duk wanda ke neman ku fito ku tayar da hankali. Tuni Najeriya ta ɗanɗana matsalolin mummunar zanga-zanga.”

Matasa na cigaba da tattaunawa game da zanga-zangar da masu shirya ta suka ce za a yi daga ranar 1 ga watan Agusta mai zuwa, musamman a shafukan sada zumunta.

Shi ma Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya nemi masu shirya zanga-zangar “su dakata tukunna har sai sun ji irin martanin zai mayar game da koke-kokensu”.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...