No menu items!

Sample Page Title

Date:

WHO na ganin babbar barazana ta yaɗuwar cutar shan inna a faɗin Gaza

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce, akwai babban haɗarin kamuwa da cutar shan inna a Gaza da ma gaba da iyakokinta, saboda yanayin rashin lafiya da tsaftar muhalli a yankin Falasɗinawa da ke fama da yaƙi.

Ayadil Saparbekov, jagoran tawagar gaggawa na kiwon lafiya a WHO a Gaza da kuma Yammacin Kogin Jordan da aka mamaye, ya ce an ware nau’in cutar shan inna ta 2 da aka samu daga samfuran muhalli daga najasa a Gaza.

“Akwai babban haɗarin yaɗa cutar shan inna da ke yaduwa a Zirin Gaza, ba wai kawai don gano cutar ba amma saboda tsananin yanayin da ake ciki na tsaftar ruwa,” kamar yadda ya shaida wa manema labarai a Geneva ta hanyar bidiyo daga Kudus.

KU KUMA KARANTA: An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

“Hakanan cutar tana iya yaɗuwa a duniya, a wani matsayi mai girma.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...