No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Kaduna ta nisanta kanta akan bidiyon dukan Ɗan-Balki kwamanda

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da umarnin gudanar cikakken bincike akan bidiyon da aka nuna ana dukan ɗan siyasar nan na Kano, Abdulmajid Ɗan Bilki Kwamanda, wanda yake yawo a kafafen sada zumunta.

A cikin wata sanawar da aka raba wa manema  labarai a Kaduna ɗai ɗauke da sa hannun babban Sakataren yaɗa labarai na gwamnatin jihar Kaduna Muhammad Lawal Shehu, ya ce  gwamnatin ta nisanta kanta aka lamarin

“An ja hankalin gwamnatin jihar Kaduna game da wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, inda aka nuna wasu da ba a san ko su wa ye ba su na yi wa Ɗan Bilki Kwamandan bulala bisa zargin shi da zagin gwamna Uba Sani”

Sanarwar ta ci gaba da cewa “Gwamnatin jihar Kaduna dai ta nisanta kan ta daga wannan mummunan lamarin, ta na mai cewa hakan ba ya da hurumi a duk wata al’umma tagari, don haka ta na nan a kan bakar ta na mutunta tsarin bin doka da oda”

KU KUMA KARANTA: Su wa suka yi wa Ɗan-Bilki Kwamanda duka?

Haka kuma, gwamnatin jihar ta bayyana cewa tsarin shugabancin ta an gina shi ne a kan adalci da daidaito da kuma mutunta ɗan Adam.

Sanarwar ta ƙara da cewa, gwamnatin jihar Kaduna ta na maraba da shawarwarin al’umma, sannann ta buɗe ƙofar ta yadda kowa zai iya bayyana ra’ayin sa a siyasance.

Ta ce Gwamnan jihar Kaduna ya kwashe tsawon lokaci ya na fafutukar kare ‘yancin ɗan Adam, don haka har yanzu ya na kan bakar sa ta tabbatar da ganin ba a tauye haƙƙin kowane bil-Adama ba bisa tsarin doka da oda.

Tuni dai Gwamna Uba Sani ya bada umurnin a gudanar da ƙwaƙƙwaran bincike a kan wannan mumman lamarin, sannan ya lashi takobin bin diddigin yadda lamarin ya faru, tare da bada tabbacin cewa duk mai hannu a aika-aikar dole ya fuskanci hukuncin abin da ya aikata.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...