Connect with us

Laifi

Ƴan sanda a jihar Yobe sun kama wata mata da kashe mijinta da wuƙa

Published

on

Abin da ya sa aka ba da belin matar da ake zargi da kashe mijinta a Damaturu - Suleiman Hassan Gimba Esq

Ƴan sanda a jihar Yobe sun kama wata mata da kashe mijinta da wuƙa

Ana zargin wata matar aure, Zainab Isa, mai kimanin shekara 22 ta kashe mijinta Ibrahim Yahaya Mai kimanin shekara 25 mazaunin unguwar Abbati cikin garin Damaturu a Jihar Yobe.

Lamarin ya faru ne sakamakon taƙaddamar da ta auku tsakanin ma’uaratan ranar Talata wadda ya kai ga ta soka wa mijinta nata wuƙa kuma nan take ya ce ga garinku nan.

Wata majiyar da ke unguwar ta Abbari ta bayyana cewar, ma’auratan sun daɗe suna takun saƙa a tsakaninsu, amma abinka da ajali taƙaddamar ƙarshen ita ce ta kai ga matar ta aika da mijin nata lahira.

Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta bakin kakakinta, DSP Dungus Abdulkarim ta tabbatar da faruwar wannan mummunan lamari.

Wakilinmu ya ruwaito cewa DSP Dungus ya yi wa manema labarai ƙarin haske kan faruwar lamarin da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar 26 ga Yuni a hedikwatar ’yan sanda ta C Division a da ke birnin Damaturu.

Kakakin ’yan sandan ya ce sun samu ƙorafin faruwar lamarin daga wani maƙwabcin ma’auratan da ke unguwar ta Abbari.

Ya ce makwabcin ya bayyana musu cewar ma’auratan sun yi musayar yawu a tsakaninsu, lamarin da ya rikiɗe zuwa rikici.

KU KUMA KARANTA: An kama wani matashi ɗan shekara 25 da laifin kashe mahaifinsa da wuƙa a Kano (Bidiyo)

Bayanai sun ce ana tsakar jayayyar ce sai matar ta yi amfani da wuƙa ta daɓa wa mijin a ƙirji, kuma daga baya ya mutu sakamakon mummunan rauni da ya samu kafin tawagar ‘yan sanda ta ƙaraso gidan.

DSP Dungus tuni aka miƙa matar sashen binciken manyan laifuffuka domin ɗaukar matakan da suka dace gabanin gurfanar da uta a gaban kuliya.

A bayanin da ta yi wa ’yan sandan, matar ta ce ba ta yi niyyar kashe mijinta ba, sai dai ta daɓa masa wuƙa ne domin ta kare kanta sakamakon dukan tsiya yake mata a lokacin faruwar lamarin duk da cewa ba ta gama samun sauƙi daga tiyatar da aka yi mata kwanan nan a dalilin haihuwar da ta yi ƙasa da wata guda.

Ta ci gaba da cewa “mun sha fuskantar matsaloli da tashin hankali a rayuwar aurenmu.

“Kusan kullum sai mun yi rikici da shi [mijin nawa] musamman idan na nemi kuɗin cefanen abinci tun lokacin aurenmu har bayan haihuwar ɗanmu na farko da na biyu.”

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Garba Ahmed, ya buƙaci ma’aurata da su riƙa miƙa rahoton  duk wani nau’i na cin zarafinsu da suke fuskanta a tsakaninsu ga mahukunta mafi kusa.

Kwamishinan ya ce wannan ita kaɗai ce hanyar da za a samu mafita mai ɗorewa ko kuma a kai ƙara kotu ko kuma miƙa wa ’yan uwa mafi kusa ƙorafi domin a yi musu sulhu maimakon ɗaukar mummunan mataki irin haka.

Ya kuma yi ƙira da umartan ’yan uwa da su riƙa  magance matsalolin da suka shafi zamantakewar aure kan lokaci don hana ta’azzara daga ƙananan rikice-rikice zuwa manya kamar kisan kai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Laifi

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Published

on

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Wani uba ya yi wa ’yarsa mai shekara 8 fyaɗe

Wani mai sayar da maganin gargajiya ya gurfana a gaban kotu bisa zarginsa da yi wa ɗiyarsa mai shekaru takwas fyaɗe.

An gurfanar da magidancin mai shekaru 35 a kan tuhume-tuhume guda na fyaɗe, wanda rundunar ‘yan sandan ta ce ya saba wa sashe na 25 (a) na dokar cin zarafin jama’a ta jihar Ondo ta shekarar 2021.

Dan sanda mai shigar da ƙara, Sufeto Martins Olowofeso, ya shaida wa kotun cewa an kama wanda ake ƙara ne a ranar 18 ga watan Yuni, 2024 bayan rahoton da aka kai ga sashin yaki da garkuwa da mutane na ’yan sanda a Alagbaka, cewa ya yi wa ’yarsa fyaɗe.

Daga bisani an tsare wanda ake tuhuma don ci gaba da bincike.

A cewar Mista Olowofeso, wanda ake zargin tare da matarsa ​​sun gudu daga gidansu bayan aikata laifin inda suka je Jihar Osun suka samo rahoton likita na ƙarya, da ke nuna babu wani abu da ya samu yarinyar.

Ya kuma shaida wa kotun cewa jami’in bincike na ’yan sanda ya sake yin wani gwaji a Akure, wanda ya nuna cewa an zakke wa yarinyar, kuma ta kwashe kwanaki uku tana zubar da jini.

A cewar Olowofeso, wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake zargin sa da shi a lokacin da jami’in da ke binciken ya yi amsa tambayoyi.

KU KUMA KARANTA: An ɗaure ɗan shekara 17 shekaru 14 a kurkuku saboda fyaɗe

Olowofeso ya buƙaci kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake ƙara a gidan gyaran hali na Olokuta har zuwa lokacin da za ta samu da shawara daga sashen shigar da kara na gwamnati (DPP).

Lauyan wanda ake ƙara, G.O Omoedu, ya shaida wa kotun cewa an kai wa wanda yake karewa sammaci ƙurarren lokaci kuma zai buƙaci lokaci domin ya mayar da martani kan batun shari’a.

Ya buƙaci kotun da ta dage ci gaba da shari’ar don ba shi damar amsa buƙatar ci gaba da sauraren ƙarar.

Majistare B.A. Alipohul ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake ƙara a hannun ’yan sanda sannan ya dage shari’ar zuwa ranar 4 ga watan Yulin 2024.

Continue Reading

Laifi

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Published

on

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

’Yan bindiga sun yi garkuwa da Hakimin Tunburku, Malam Ashiru Sherehu da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewar, maharan sun yi awon gaba da Sherehu a kan hanyarsa ta dawowa daga gona a ranar Asabar.

’Yan bindiga sun addabi yankin da ke gundumar Fatika a ‘yan kwanakin nan da hare-hare.

A cewar wani mazaunin yankin, Ahmadu, manoma ba sa iya zuwa gonakinsu da ke da nisan kilomita kaɗan daga garin saboda tsoron kada a kashe su ko kuma a sace su.

Wani basaraken gargajiya a yankin kuma Sarkin Fadan Galadimawa, Husseini Umar, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an yi garkuwa da hakimin ƙauyen da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Asabar.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

“Yana dawowa daga gonarsa da ke Tunburku sai ‘yan bindigar suka tare shi suka tafi da shi. Har yanzu ba mu ji daga gare su ba; kuma ba su tuntuɓe mu ba,” in ji shi.

A cewar Hussaini, an kuma sace wasu manoma biyu a yankin Sabon Layi da ke gundumar Kidandan a lokacin da suke aiki a gonakinsu a ranar Lahadi da rana.

Ya bayyana cewar mutanen ƙauyen da lamarin ya faru a gabansu sun kasa yin komai saboda ’yan bindigar na ɗauke da makamai.

Umar, ya koka kan yadda ’yan bindiga ke yi wa manoma ɗauki ɗai-ɗai a yankin.

Amma, ya yaba da ƙoƙarin sojojin da aka tura yankin, sai dai ya roƙi gwamnati da ta aike da ƙarin jami’an tsaro masu yawa saboda yadda rashin tsaro ke ƙara ta’azzara a yankin.

Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ba ta ce komai kan faruwar lamarin ba.

Jin ta bakin kakakin rundunar, ASP Mansir Hassan, ya ci tura domin ba ya amsa ƙiran waya.

Continue Reading

Labarai

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Published

on

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Daga Ibraheem El-Tafseer

Aƙalla mutane shida ne suka mutu inda wasu 15 suka jikkata a wani harin ƙunar baƙin wake da aka kai a garin Gwoza na jihar Borno.

Wani abin takaici ya faru ne a lokacin da ‘yar ƙunar baƙin wake ta tayar da bam a garin Gwoza, ranar Asabar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, (NAN), ya ruwaito cewa an kai harin ne a wani wurin shaƙatawa na motoci da ake ƙira Marrarraban Gwoza.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Borno Yusuf Lawal ya tabbatar da faruwar harin yana mai cewa wata ‘yar ƙunar baƙin wake ce ta kai harin.

Lawal ya ce jami’in ‘yansandan shiyyar Gwoza ne ya sanar da shi cewa aƙalla mutane shida ne suka mutu inda aka kwashe wasu 15 zuwa asibiti.

Wani ganau mai suna Buba, ya shaida wa NAN cewa ‘yar ƙunar baƙin waken ta nufi tsakiyar wani bikin aure ne, inda ta tayar da bam ɗin a nan.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Buba ya ce harin ya rusa farin ciki da murnar wannan rana ta musamman, inda ya bar iyalai da ‘yan uwa cikin makoki.

Wani wanda ya shaida lamarin, Muhammed Kasim, ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana.

“Mun ji ƙarar fashewar abubuwa, tare da ƙura, sai muka ga gawarwaki a ƙasa.”

Ya ce an kwashe da dama daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibiti yayin da aka tura jami’an tsaro domin dawo da zaman lafiya a yankin. (NAN).

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like