Connect with us

Labarai

Sojoji sun kama ɗan ta’adda Baleri, uban gidan Bello Turji

Published

on

Sojoji sun kama ɗan ta’adda Baleri, uban gidan Bello Turji

Sojoji sun kama ɗan ta’adda Baleri, uban gidan Bello Turji

Sojojin haɗin gwiwa sun kama Beleri, ƙasurgumin ɗan bindigar Najeriya da ake nema ruwa a jallo.

Baleri uban gida ne ga ƙasurgumin ɗan bindiga Bello Turji, wanda ya addabi al’ummar yankunan Jihar Zamfara da hare-haren ta’addanci da kuma satar mutane domin karɓar kuɗin fansa.

Baleri wanda shi ma ɗan Zamfara ne ya jima yana addabar al’ummar jihar da ma wasu yankunan Nijar, musamman jihar Maraɗi.

Shi ne na 40 a jerin ’yan ta’adda da hukumomin Najeriya ke nema ruwa a jallo, har ta yi alkawarin lada mai tsoka ga duk wanda ya taimaka aka kamo shi.

Sojojin na Nijar sun sanar cewa an kama Beleri ne a garin Rigar Kowa Gwani da ke yankin Gidan Rumji na jihar Maraɗi a ƙasarsu.

KU KUMA KARANTA: Jiragen yaƙin Najeriya sun yi luguden wuta a sansanonin ƴan ta’adda a Zamfara

Rundunar sojin Nijar ta ce dakarun Runduna ta Musamman mai suna Farautar Bushiya sun yi nasarar kama Beleri ne da misalin ƙarfe 1 a kan iyakar ƙasashen biyu, a jihohin Zamfaran Najeriya da kuma Maraɗin Jamhuriyar Nijar.

An kama shi ne a lokacin ya yake tsaka da  ganawa da yaransa a shirinsu na kai hari a Najeriya da Nijar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Published

on

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Rikicin Masarauta: Aminu Ado ya ɗaga tuta a fadar Nassarawa

Daga Muhammad Kukuri

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya ɗaga tutar mulki a ƙaramar fadar da ke unguwar Nassarawa inda yake zaune.

A bisa al’ada, tutar na zama ne a matsayin alamar iko, kuma daga ta na alamta cewa sarki yana cikin fada.

Wannan kuwa na zuwa ne duk da umarnin gwamnatin Kano ga Sarki Aminu ya fice daga fadar a yayin da ake ci gaba da dambarwar sarautar Kano.

Akan daga tutar ce da misalin karfe 6 na safe a kuma sauke ta 6 na yamma ko idan sarki ya yi bulaguron aiki.

Neptune Prime Hausa ta gano cewa ba a ɗaga tutar ba a Fadar Nassarawa ba sai a safiyar Alhamis, duk da cewa an sanya karfenta a safiyar Laraba.

An yi ta ji-ta-ji-ta ranar Laraba cewa an sanya tutar, amma mun gano cewa kafen kawai aka sa, Alhamis da safe kuma aka daga tutar.

Daga tutar a karamar Fadar Nassarawa na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da shari’ar da Gwamnatin Kano ke neman kotu ta hana Aminu Ado Bayero Aminu gabatar da kansa a matsayin Sarkin Kano bayan ta maye gurbinsa sa Muhammadu Sanuni II, Sarkin Kano na 16.

Gwamnatin jihar ta je kotu ne tana neman a hana duk sarakuna biyar da ta rushe masarautunsu a jihar gabatar da kansu a matsayin sarakunan masarautun.

Continue Reading

Labarai

Majalisa ta amince a tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2023

Published

on

Majalisa ta amince a tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2023

Majalisa ta amince a tsawaita wa’adin aiwatar da kasafin kuɗin 2023

Daga Muhammad Kukuri

Majalisar Wakilai ta amince da buƙatar ci gaba da aiwatar da kasafin ƙuɗin 2023 har zuwa ƙarshen shekarar 2024.

Hakan dai na kunshe ne cikin ata sanarwa da majalisar ta fitar ta hannun shugaban kwamitin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a, Akin Rotimi.

Ya bayyana cewa, “an amince da ƙudurin ne domin amfanin ƙasa baki ɗaya, bayan zazzafar muhawara da aka tafka kan lamarin.”

Sanarwar ta ce “Majalisar wakilai ta amince da dokoki biyu waɗanda suka buƙaci tsawaita aiwatar da kasafin kuɗi na 2023 da kuma ƙaramin kasafin kuɗi na shekarar ta 2023 har zuwa watan Disamban 2024.”

KU KUMA KARANTA: El-Rufai ya kai ƙarar Majalisar Dokokin Kaduna kotu

Ana iya tuna cewa dai Shugaba Bola Tinubu ne ya tura ƙudurorin biyu zuwa majalisar dokoki.

A lokacin muhawara kan ƙudurorin, wasu ’an majalisa sun nuna shakku game da buƙatar amincewa da su cikin sauri, inda suka yi fargabar kada ya kasance akwai wani abu da zai cuci al’ummar ƙasa.

Daga cikin waɗanda a farko suka yi tirjiya kan aiwatar da ƙudirin har da shugaban marasa rinjaye na majalisar, Kingsley Chinda da tsohon bulaliyar majalisar, Alhassan Ado Doguwa.

Sai dai bayan tattaunawa da kuma duba ɓangarorin dokar a matakin kwamiti, zauren majalisar ya sake zama inda ya amince da ƙudurorin.

Continue Reading

Labarai

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi – Hajiya Aisha Ibrahim (Bidiyo)

Published

on

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi - Hajiya Aisha Ibrahim

Halin da na shiga bayan karɓar kwangilar abincin bogi – Hajiya Aisha Ibrahim (Bidiyo)

Wata mata mai gidan abinci ta faɗa tarkon ’yan damfara inda aka ba ta kwangilar bogi ta samar da abinci na kwanaki uku kan kuɗi Naira miliyan 13.

An ba Hajiya A’isha Ibrahim kwangilar bogin ce da sunan za ta ciyar da mabuƙata dubu tara a ƙananan hukumomi uku na jihar.

Labarin Hajiya Aisha da ke sana’ar abinci a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi ya karaɗe gari ne bayan ta yi bidiyon halin da take ciki a kafofin sada zumunta.

Hakan ya sa gwamnan jihar, Sanata Bala Abdulqadir Muhammad ya shiga tsakani ya biya ta kuɗin data kashe wajen yin abincin, aka karɓi abincin aka raba wa masu buƙata.

A zantawar datayi da manema labarai, Hajiya Aisha ta ce wani mutum ne ya tuntuɓe ta da ya ba ta kwangilar samar da abinci ga mutane 9,600 a ƙananan hukumomin Bauchi, Alkaleri, da Kirfi.

A yayin da take bayyana irin halin da ta shiga, duk da cewa ba ta bayyana sunan mutumin da ya ba ta kwangilar bogin ba, Hajiya Aishah ta ce mutumin ya ba ta tabbacin cewa nan ba da daɗewa ba za a rattaba hannu kan yarjejeniyar kwangilar, kuma ba za a saka ta cikin hadari ba.

“Ya dage cewa in ci gaba da kwangilar saboda ba a sanya hannu kan yarjejeniyar ba, amma za a ba ni takardan yarjejeniyar yin kwangilar lokacin da aka sanya hannu,” inji Aisha.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin tarayya za ta fara farautar ma’aikatan da suke da shaidar karatun bogi

Ta ce ta amince da tabbacin da ya ba ta saboda ta san yadda kungiyoyi masu zaman kansu suke yi, in suka bada irin wannan aiki, kuma suna biya bayan an kammala aikin.

Daga nan sai ta saki zuciyarta ta ci gaba da bin umurnin mutumin ta samo ma’aikata ta suka kwana suna aikin yin abinci.

Ta ce da suka kammala sai ta ƙira mutumin da nufin ta san waɗanda za su karɓi abincin, sai ya ce ta jira yana jiran a ba shi umurni tukuna.

“Bayan karfe 1 na rana ban ji ɗuriyarsa ba, sai na tafi ofishinsa, ya ce in jira yana jiran umarni.
“Bayan uku na yamma na fara ƙiran sa sau da yawa, amma ba ya ɗauka.

“Da muka je ofishinsa da mijina da misalin karfe biyar na yamma, sai aka ce mana ba ya nan.
“Tun daga lokacin ya ƙi ɗaukar wayata har ƙarfe biyar na yammaci.”

Hajiya A’isha ta ce ta yi matukar kaɗuwa da lamarin domin ta karɓi basussuka ne ta yi abincin.

Da ta kasa samun mutumin, sai ta shiga kafafen sada zumunta tana neman taimako.

Ta ce “Kwamishiniyar jin ƙai da bada agaji na Jihar Bauchj Hajiya Hajara Yakubu Wanka ta ƙira ni inda ta ce Gwamna ya ga bidiyona a intanet kuma ya umarce ta da ta biya ni diyya.

“Ina godiya ga Gwamna Bala Mohammed kan matakin da ya ɗauka na ceto ni cikin gaggawa.”
Hajiya Aisha ta ce gwamnati ta biya kuɗin da ta sayi kayan Naira miliyan 7.5 ba, kuma ta karɓi abincin aka rarraba shi wa masu bukata.

Da yake mayar da martani kan lamarin, babban sakatare a ma’aikatar, Alhaji Shuaibu Alhaji Muhammad, ya bayyana cewa asalin kuɗin kwangilar naira miliyan 13 ne, amma gwamnatin jihar ta biya diyya na ainihin kuɗin kayan abinci da Hajiya Aisha ta saya.

Wani abu daya ja hankalin jama’a shi ne Hajiya Aisha ta zabi kada ta bayyana sunan mutumin da ya yaudare ta, duk da cewa ta yi wa jami’an tsaro cikakken bayani.

Ta kuma gargaɗi jama’a game da masu zamba a asusun banki da za su ce za su rika neman tallafi da sunanta.

Kalli bidiyo a nan:

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like