No menu items!

Sample Page Title

Date:

Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin jirgin samanta

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin sufurin jirgin samanta na Air Nigeria, har sai Baba ta gani.

Ministan Sufurin Jiragen Sama Festus Keyamo, ne ya sanar da hakan yayin taron Ministoci na cika shekarar Tinubu, guda a kan mulkin ƙasar.

Ya ce, matakin ya zo ne, lura da cewa kamfanin a ko da yaushe yunkurin yin amfani da jiragen saman wasu ƙasashen waje ya ke a matsayin na ta.

Idan za a iya tunawa, a shekarar 2023 ne, ma’aikatar sufurin jiragen sama, ƙarƙashin jagorancin tsohon ministan sufuri, Hadi Sirika, ta ƙaddamar da kamfanin jirgin mallakin Najeriya, wato Nigerian Air kwanaki uku kafin ƙarshen wa’adin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.

Lamarin dai ya yanwo cece-kuce a tsakanin al’ummar ƙasar, la’akhari da yadda daga bisani aka gane cewa akwai kuskunda a cikin batun.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...