Connect with us

Labarai

Gwamnan Kano ya ba da umarnin kama Aminu Ado Bayero

Published

on

Gwamnan Kano ya ba da umarnin kama Aminu Ado Bayero

Gwamnan Kano ya ba da umarnin kama Aminu Ado Bayero

Gwamnan Jihar Kano ya ba da umarnin kama Alhaji Aminu Ado Bayero saboda zargin yunƙurin tayar da tarzoma a jihar bayan sanar da sauke shi daga sarautar Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da umarnin ne raanar Asabar da safe ta hannun daraktansa na yaɗa labarai Sanusi Bature Dawakin Tofa.

Abba Kabir ya ce Aminu Ado “ya shiga Kano cikin daren da ya gabata, don shiga fadar Kano da ƙarfin tsiya kwana biyu bayan sauke shi daga sarauta.”

“Bisa haka ne gwamnan ya ba da umarnin kama tuɓaɓɓen Sarkin nan-take saboda kawo tsaiko a zaman lafiyar al’umma da kuma yunƙurin rusa kwanciyar hankalin da ake da shi a Kano,” a cewar sanarwar.

Ranar Juma’a da tsakiyar dare ne Alhaji Aminu Ado Bayero ya sauka a filin jirgin sama na Malam Aminu da ke Kano, daga nan ya zarce Gidan Sarki na Nasarawa, wanda ke da nisan kimanin kilomita ɗaya daga Gidan Gwamnatin Jihar Kano.

A ranar Juma’a ne Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bai wa Muhammadu Sanusi II takardar kama aiki a matsayin sabon Sarki, kwana ɗaya bayan sa hannu a gyaran dokar Masaratun Kano ta 2024, wacce ta rushe masarautun jihar biyar ta kuma sauke sarakunan jihar, kamar yadda gwamnan ya ce.

A jawabin da ya gabatar ranar Juma’a lokacin miƙa wa Muhammadu Sanusi II takardar a fadar Gwamnatin Kano, Gwamna Abba ya ce Sarki Sanusi zai ci gaba da zama a masaukinsa ana ci gaba da al’umuran sarauta, har zuwa wani lokaci.

Sai dai ranar Juma’a da tsakar dare Sarki Sanusi II ya shiga fadar ta Kano bisa rakiyar tsohon gwamnan Kano Rabiu Kwankwaso da Gwamna Abba Kabir Yusuf da mataimakinsa da shugaban majalisa da wasu ƙusoshin gwamnati.

Matakin ya biyo bayan raɗe-raɗin cewa Alhaji Aminu Ado Bayero yana shirin komawa Kano sannan ya shiga Gidan Sarauta, kamar yadda Mataimakin Gwamnan Jihar Kwamared Aminu Abdussalam ya sanar da safiyar Asabar.

Ya yi gargaɗin cewa za su ɗauki duk wani mataki na ganin cewa naɗin da aka yi wa Sarki Muhammadu Sanusi II ya tabbata.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Abba Kabir ya mayar da Muhammadu Sanusi II Sarautar Kano

Mataimakin gwamnan ya bayyana haka ne yayin da yake zanta wa da ‘yan jarida da safiyar Asabar a fadar Masarautar Kano.

Ya zargi wasu da ke kusa da gwamnatin tarayya da yin amfani da jami’an tsaro wajen “ganin cewa an tanƙwara an banƙara a kan buƙatar al’ummar jihar Kano an kawo musu abin da ba shi suke buƙata ba.”
“Wannan shi ne abin da ya kawo mu yau.”

“Sabon Sarkin Kano Alhaji Sanusi Lamido Sanusi ya karɓi takardarsa ta kama aiki, kuma muna kawo shi nan gidan, muna zagaya gidan da shi,” kamar yadda ya shaida wa ‘yan jarida a fadar Sarkin Kano.

Ya ƙara da cewa duk wasu manya na gwamnati Kano suna fadar Sarki, kuma za su kasance a fadar har sai komai ya daidaita.

“Gwamna ne ma gaba ɗaya da gwamnati muka zo muka rako Mai Martaba Sarki da shugaban majalisar da ‘yan majalisa,” in ji shi.

Ya zargi waɗanda suke son mayar da Sarki Aminu da yunƙurin dagula al’amura a Kano.
“Mun kasa gane me ake so a yi… a ɓata duk abin da za a ɓata… saboda ba jihar su ba ce?

Sai dai har kawo yanzu babu wani martani daga gwamnatin tarayyar ƙasar kan abin da ke faruwa a Kano da kuma zarge-zargen gwamnatin ta Kano.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like